Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta buƙaci gwamnatin ƙasar ta jinkirta aiwatar da dokokin haraji da aka yi wa gyara saboda zargin an cusa wasu tanade-tanade da a basu cikin dokokin da majalisa ta zartar.
Kakakin jam'iyyar ADC, Bolaji Abdullahi ya zargi gwamnati da yi wa sassa da dama na dokokin harajin, ciki harda tanadin bai wa shugaban ƙasa ikon kama duk wanda bai yi biyayya ga dokokin harajin ba, da kuma ƙwace ƙaddarorinsa.
“ADC na kiran a gaggauta dakatar da batun aiwatar da dokokin harajin 2025 da shugaba Bola Tinubu ya sanya wa hannu omin bayar da dama ga ƴan majalisa su gudanar da cikakken nazari a kai,'' in ji Bolaji Abdullahi.
ADC ta ce wannan kira ya zama wajibi saboda tantance zargin da ya biyo bayan bankaɗar da aka yi, da ta gano yadda aka yi cushen wasu ƙa'idoji a cikin dokokin harajin, duk da cewa majalisar dokokin tarayya ta riga ta kammala aiki a kai.
Jam;iyyar adawar ta ce irin wannan mummunar hanya ce aka ɗauka wadda ke barazana ga tanadin rabon ƙarfin iko da bibiyar ayyukan juna tsakanin ɓangaren zartarwa da na dokoki da kuma na shari'a a Najerya.
A cikin watan Yuni shugaba Tinubu ya sanya hannu kan dokokin harajin da aka yi wa gyara, bayan shafe watanni ana muhawara mai zafi a zauren majalisun ƙasar biyu, da kuma a tsakanin jama'ar ƙasar.
Amma a ƴan kwanakin nan, wani ɗan majalisar wakilai daga jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya ja hankalin majalisar cewa dokar da ake shirin fara aiwatarwa a ranar ɗaya ga watan Janairun 2026 ta yi hannun riga da wadda majalisar ta zartar ta kuma aikewa shugaban ƙasa.