Gwamnatina ba za ta lamunci rashawa ba - Ahmed Aliyu
Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya "gargaɗi" manyan ma'aikatan gwamnatin jihar game da rashawa, tare da bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.
Wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama'a na gwamnan jihar Abubakar Bawa ya fitar, ta ce gwamnan ya yi wannan bayani ne sa'ilin taron buɗe-baki da manyan sakatarori da shugabannin ma'aikatu da kuma daraktocin gwamnatin jihar a ranar Litinin.
Aliyu ya ce "a matsayinku na shugabanni a ma'aikatunku, wajibi ne ku rungumi ɗabi'ar kaffa-kaffa da adalci a kan duk wata hulɗa."
Sanarwar ta kuma ja hankalin ma'aikata kan zuwa aiki latti da kuma ƙin zuwa aikin baki ɗaya.
Ya ce gwamnatinsa za ta ɗauki matakan inganta walwalar ma'aikata, saboda haka ya kamata su ma, su saka mata ta hanyar mayar da hankali wajen aiki.