A jamhuriyar Nijar, a yau Litinin ne gwamnatin mulkin sojan ƙasar ta ware domin gudanar da azumi a faɗin ƙasar.
Zaman majalisar ministoci na ƙarshen mako ne ya umurci al'ummar ƙasar da su gudanar da azumin na yau tare da addu'o'in Allah ya ba ƙasashen AES nasara a yaƙin da suke yi da ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai.
Yanayin tsaro a yankin Sahel na ci gaba taɓarɓarewa yayin da masu iƙirarin jihadi ke ƙara matsa lamba kan sojojin ƙasashen.
Ƙasashen uku da suka haɗa da Nijar da Mali da Burkina Faso na ƙara fuskantar matsala wajen aiwatar da iko a kan dukkanin yankunansu, har ma ya kai wasu yankuna sun faɗa hannun ƴan bindigar.
Lamarin ya sake ta'azzara ne bayan harin haɗin gwiwar da masu iƙirarin jihadi suka kai a Mali a ƙarshen watan da ya gabata.
A jamhuriyar NIjar, bayan matakan sojin da gwamnatin mulkin soji ta ce tana ɗauka a yayin zaman majalisar a ƙarshen mako, ta kuma buƙaci ƴan ƙasar da su duƙufa yin addu'oi domin nasara a kan abokan gaba
Wasu ƴan ƙasar dai sun bayyana ra'ayoyinsu inda suka ce suna fatan azumin ya zama karɓaɓɓe, inda wasu suka ce dama sukan yi azumin, kuma idan hakan bai saɓawa addini ba za su yi.