Akwai masu cin amanar ƙasa a majalisar Amurka - Trump

Asalin hoton, Getty Images
Shugaba Trump ya bayyana wasu 'yan majalisar Amurka na jam'iyar Democrat a matsayin masu cin amanar kasa, da kuma ya dace a yanke wa hukuncin kisa.
'Yan majalisar sun bukaci jami'an sojin kasar su bijirewa duk wani umurnin kai hari wata kasa da ya sabawa doka.
Mista Trump ya wallafa a shafinsa na sada zumunta yana zargin 'yan siyasar shida da cewa sun yi kalaman da ya dace a dauki mataki mai tsauri a kansu ta hanyar zaratas musu da hukuncin kisa.
'Yan majalisar na jam'iyyar Democrats sun fitar da wani bidiyo kwanan nan inda suke cewa kundin tsarin mulkin Amurka na fuskantar barazana.
To sai dai ba su yi karin haske akan umurnin da suka nemi a bijirewa ba.


















