Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 29 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed da Aisha Babangida

  1. 'Mozambique ta fuskanci ambaliya mafi muni a bana a shekara 25'

    Hukumomi a Mozambique sun bayyana cewa ambaliyar ruwa mai tsanani da ta afka wa sassan ƙasar tun daga ranar 7 ga Janairu ita ce mafi muni a shekara 25.

    Ambaliyar ta kashe aƙalla mutum 18, ta tilasta wa kimanin mutum 392,000 barin muhallansu, yayin da kusan mutum 780,000 ne ambaliyar ta shafa a faɗin ƙasar tun bayan fara damina a watan Oktoban 2025, a cewar gwamnati da Majalisar Ɗinkin Duniya.

    Jihohin Gaza da Maputo da Sofala ne ambaliyar ta fi shafa inda gidaje da makarantu da cibiyoyin lafiya da hanyoyi da wutar lantarki suka lalace matuƙa.

    Hukumar kula da bala’o’i ta ƙasa (INGD) ta yi gargaɗin cewa adadin mutanen da ambaliyar ta shafa na iya kai wa miliyan 1.1, tana mai kiran lamarin mafi muni cikin shekaru fiye da ashirin.

    Manyan koguna irin su Limpopo da Incomati da Save sun cika tam inda suka yi ambaliya, lamarin da ya katse al’umma da dama tare da haifar da ƙarancin abinci da man fetur.

    Rahotanni sun nuna cewa fiye da gidaje 150,000 da cibiyoyin lafiya 242 da makarantu sama da 575 sun nutse, yayin da sama da hanyoyin kilomita 5,000 sun lalace, ciki har da rushewar wasu sassan babbar hanyar da ke haɗa arewa da kudu.

    Shugaban ƙasar, Daniel Chapo, ya tura jami’an agaji da sojoji da motocin gwamnati domin kai ɗauki, tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyin jin ƙai.

  2. Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya - Sanata Ningi

    Sanata Abdul Ahmed Ningi, mai wakiltar Bauchi ta Tsakiya, ya bayyana damuwa kan yadda Amurka ta kai hare-haren sama kan wuraren ‘yan ta’adda a Jihar Sokoto ba tare da neman izini ko tuntuɓar majalisar dokokin ƙasar ba kafin ta kai harin.

    Sanatan ya ce "hakan ya saɓa wa ikon ƙasar tare da karya tsarin sa ido na majalisa kan al’amuran tsaro."

    Sanata Ningi ya tayar da batun ne a zauren majalisar dattawa inda ya ce "majalisar dokoki na da rawar da doka ta tanada a harkokin tsaro da kuma shigar sojojin ƙasashen waje, amma ba a nemi ra’ayinta ba kafin kai harin."

    Ya gargaɗi cewa "barin ɓangaren zartarwa ya yanke irin wannan hukunci shi kaɗai na iya buɗe ƙofa ga wasu ƙasashe su ma su ɗauki mataki makamancin haka nan gaba."

    Biyo bayan wannan ƙorafi ne shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa Majalisar ta shirya gudanar da zama domin tattaunawa da yan majalisa kan lamarin.

    Ya ce an shirya yin bayanin tun da farko amma aka ɗage shi domin girmama marigayi Sanata Godiya Akwashiki.

    Akpabio ya jaddada cewa batun tsaro ne mai matuƙar muhimmanci wanda bai dace a tattauna a bainar jama’a ba, yana mai tabbatar da cewa za a shirya zama nan ba da jimawa ba domin yi wa sanatoci bayani kan hare-haren da Amurka ta kai a ranar 25 ga Disamba 2025, wanda AFRICOM ta ce an aiwatar da shi tare da haɗin gwiwar hukumomin Najeriya domin kai farmaki kan sansanonin ‘yan ISIS.

  3. Komawar Abba APC: Wa ke da riba wa ke da asara?

    Komawar Gwamnan jihar Kabo, Abba Kabir Yusuf jam'iyyar APC na ci gaba da ɗaukar hankali a siyasar arewacin Najeriya.

    Yayin da wasu ke ci gaba da murna wasu kuma takaici matakin ya janyo musu, sakamakon abin da matakin gwamnan ya janyo musu.

    Gwamnan dai ya ce ya zaɓi komawa APC ne saboda ci gaban al'ummar Kano.

    Yayin da yake jawabi a wurin taron komawar tasa, Abba Kabir ya ce ya ɗauki matakin ne domin jihar Kanio ta amfana da manyan ayyukan gwmanatin tarayya.

    Matakin gwamnan zai sauya abubuwa masu yawa a fagen siyasar Kano da ma Najeriya baki ɗaya.

    Yayin da matakin zai yi wa wasu da dama daɗi, wasu kuwa akasin hakan ne, saboda ba yadda suka so ba.

    BBC ta yi nazarin ɓangarorin siyasa da za su ƙirga riba ko asara saboda matakin an gwamnan Kano.

  4. An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

    A daren jiya ne aka ji ƙarar harbe-harbe da fashe-fashe a kusa da kusa da filin jirgin sama na ƙasa da ƙasa na Diori Hamari da ke babban birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

    Kafar LSI Africa ce ta ruwaito labarin daga wasu shaidun gani da ido, inda suka ce an fara jin ƙarar ne da misalin ƙarfe 12 na dare, sannan ya ɗan ɗauki lokaci ana yi.

    Wasu faye-fayen bidiyo da suka karaɗe kafofin sada zumunta a ƙasar sun nuna yadda haske ya yi sama daga daidai yankin da ake jin harbe-harben.

    Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton dai hukumomi a ƙasar ba su ce komai ba kan aukuwar lamarin, musamman kan musabbin harbe-harbe da fashe-fashen ko asarar da aka yi, da kuma ko an rasa rai.

    Sai dai akwai rahotannin da ba a tabbatar ba da ke zargin wataƙila mayaƙa masu iƙirarin jihadi ne suka yi yunƙurin kai hari a filin jirgin.

    Sai dai wasu na zargin ganin yanayin ƙarar wataƙila akwai yiwuwar wata matsala ce ta cikin gida da ba za ta rasa nasaba da boren sojoji ba, kamar yadda rahoton ya ƙara.

    Nijar dai na fama da matsalolin rashin tsaro a cikin ƴan shekarun nan duk da cewa tana ƙarƙashin mulkin Janar Abdourahmane Tchiani, wanda ya karɓi mulki bayan juyin mulkin watan Yulin 2023.

  5. Jirgin ruwan sojin Amurka na tunkarar Iran - Trump

    Shugaba Trump ya sake yi wa Iran barazanar ɗaukar matakin soja, inda yake matsa wa ƙasar lamba don ta tattauna kan yarjejeniyar makaman nukiliya.

    Mista Trump ya ce wani babban jirgin rundunar sojin Amurka na tunkarar ƙasar, yana mai barazanar cewa harin da zai kai mata nan gaba zai nunka irin wanda ya kai mata a watan Yuni.

    Iran ta dage cewa shirinta na nukiliya na zaman lafiya ne, tana mai gargaɗin cewa duk wani hari da Amurka ta kai mata na iya jefa rayukan dukkan dakarunta da ke gabas ta tsakiya cikin haɗari.

    A Majalisar Dinkin Duniya, China ta yi gargadi game da barazanar ta Amurka. Wannan na faurwa ne bayan zargin kisan dubban masu zanga-zangar adawa da gwamnati da aka yi a Iran.

  6. Buɗewa

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.