Trump ya buƙaci Iraniyawa su ƙwace gwamnatin ƙasar
Shugaban Amurka Donald Trump ya buƙaci Iraniyawa su yi amfani da manyan hare-haren Amurka da Isra'ola wajen kifar da gwamnatin ƙasar.
Cikin wani jawabi da ya yi ta bidiyo, Mista Trump ya ce ''Idan muka gama namu, ku kuma ku ƙwace gwamnatin, taku ce, ina ganin wannan ce damar da kuka samu ta yin hakan''.
Ya kuma faɗa wa dakarun sojin Iran cewa za a ba su ''kariya'' idan suka amince su ajiya makamansu, ko kuma su ''fuskanci mutuwa''.
A farkon watan Janairu ne Trump ya yi barazanar kai harin bom kan Iran saboda yadda jami'anm tsaron ƙasdar ke far wa masu zanga-zangar adawa da gwamnati, wadda ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta ce an kashe mutum 6,480.