Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 28/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 28/02/2026

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Trump ya buƙaci Iraniyawa su ƙwace gwamnatin ƙasar

    Shugaban Amurka Donald Trump ya buƙaci Iraniyawa su yi amfani da manyan hare-haren Amurka da Isra'ola wajen kifar da gwamnatin ƙasar.

    Cikin wani jawabi da ya yi ta bidiyo, Mista Trump ya ce ''Idan muka gama namu, ku kuma ku ƙwace gwamnatin, taku ce, ina ganin wannan ce damar da kuka samu ta yin hakan''.

    Ya kuma faɗa wa dakarun sojin Iran cewa za a ba su ''kariya'' idan suka amince su ajiya makamansu, ko kuma su ''fuskanci mutuwa''.

    A farkon watan Janairu ne Trump ya yi barazanar kai harin bom kan Iran saboda yadda jami'anm tsaron ƙasdar ke far wa masu zanga-zangar adawa da gwamnati, wadda ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta ce an kashe mutum 6,480.

  2. Iran ta ƙaddamar da hara-haren ramuwar gayya

    Iran ta ƙaddamar da hare-haren ramuwar gayya game da hare-haren da Isra'ila da Amurka suka kai mata da safiyar yau.

    Cikin wata sanarwa da rundunar sojin Isra'ila, IDF ta fitar, ta tabbatar da gano makamai masu linzami da Iran ta harba cikin Isra'ila, amma tana ƙoƙarin ganin ta kakkaɓo su.

    Haka ma Qatar ta tabbatar da cewa Iran ta kai hari kan wasu sansanonin sojin Amurka da ke ƙasaer, kodayake ta ce an kakkaɓo hare-haren.

    Ita ma ƙasar Bahrain ta tabbatar da kai hari kan sansanonin sojin ruwan Amurka da ke ƙasar, kodayake ba ta alaƙanta harin da kowace ƙasa ba.

  3. Mun gaji da batun yarjejeniya - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Amurka ta gaji da batun yarjejeniyar nukiliyar Iran.

    Cikin wani bidiyon minti takwas da ya fitar a shafinsa na sada zumunta, shugaban na Amurka ya tabbatar da hannun AMurka a harin Iran.

    Ya tabbatar da cewa Amurka ta ƙaddamar da ''babban faɗa'' da Iran.

    ya ƙara da cewa ''Za mu wargaza makamanta masu linzami tare da lalata kamfanin ƙera makamanta da ke ƙarƙashin ƙasa...''

  4. Biranen Iran biyar da hare-haren suka faɗa

    Kamfanin dillancin labaran Iran na Fars ya bayar da rahoton birane biyar da aka samu faɗawar hare-hare a cikinsu.

    Biranen sun haɗa da Isfahan da Qom da Karaj da Kermanshah da kuma babban birnin ƙasar Tehran

  5. Hotunan yadda yahaƙi ke tashi a Iran bayan harin Isra'ila da Amurka

  6. Isra'ila da Iran sun rufe sararin samaniyarsu

    Isra'ila ta sanar da rufe sararin samniyartya bayan harin da haɗa gwiwa da Amurka suka kai wa Iran da safiyar yau Asabar, a cewar kafofin yaɗa labaran ƙasar.

    Can a Iran kamfanin dillancin labarai na Tasnim mai alaƙa da dakarun juyin juya halin ƙasar, ya bayar da rahoton cewar Iran ta rufe sararin samaniyarta.

    Ana sa Iran za ta ƙaddamar da harin ramuwar gayya kan Isr'ila da sansanonin sojin AMurka da ke gabas ta tsakiya.

  7. Amurka da Isra'ila sun ƙaddamar da hare-hare kan Iran

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce an ji ƙarar manyan abubuwan fashewar uku a birnin Tehran.

    Kamfanin dillancin labarai na Fars ya ce ya samu rahatonnin faɗawa makamai masu linzami a babban birnin Iran.

    Kafofin yaɗa labaran Amurka da na Isra'ila sun ce Amurka da Isra'ila ne suka haɗa gwiwa wajen ƙaddamar da harin.

    Dama dai Amurka ta jima tana barazanar far wa Iran da yaƙi saboda shirinta na nukiliya.

    A makon da ya gabata Shugaba Trump na Amurka ya bai wa ƙasar wa'adin kwana 10, don ta cimma yarjejeniya ko ta ɗauki matakin soji a kanta.