KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 28/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 28/02/2026

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Bidiyon yadda Iran ta kai hari sansanin sojin Amurka da ke Bahrain

    Bidiyoyin harin ramuwar gayyar Iran a yankin Gabas ta Tsakiya na ci gaba da ɓulla.

    Akwai sansanonin sojin amurka masu yawa a yankin gabas ta Tsakiya, da za a iya kai wa hari.

    Bahrain na ɗaya daga ƙasashen yankin Gulf da dama da Iran ta kai wa hari bayan hare-haren amurka da Isra'ila a ƙasarta.

    Iran ta kai hari babban sansanin sojin ruwan Amurka da ke ƙasar ta Bahrain.

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon
  2. Iran na kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya

    ..

    Asalin hoton, ..

    Rundunar sojin Qatar ta tabbatar da hare-haren Iran a ƙasar - inda Amurka ke da sansanin sojin sama na Al-Udeid, mafi girma da take da shi a Gabas ta tsakiya.

    Sai dai ƙasar ta ce ta samu nasarar kakkaɓo hare-haren.

    Can ma a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa hukumomin ƙasar sun tabbatar da mutuwar mutum guda bayan kakkaɓo harin Iran a ƙasar.

    Haka ma hukumomin Bahrain sun tabbatar da hari kan sansanon sojin ruwan Amurka da ke ƙasar, kodayake ba ta alaƙanta harin da kowace ƙasa ba.

    Ita ma ƙasar Kuwait ta ce ta kakkaɓo harin Iran da ya tunkari sansanin sojin Amurka da ke ƙasar.

  3. Netanyahu: Ba za mu bari Iran ta mallaki nukiliya ba

    Netanyahu

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Netanyahu

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce bai kamata a bar gwamnatin Iran ta mallaki makamin nukiliya ba.

    Cikin wata sanarwa da ya fitar bayan harin haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila kan Iran, Netanyahu ya gode wa Amurka game da harin.

    ''Cikin shekara 47 gwamnatin Ayatollah na ambata mutuwa ga Isra'ila da mutuwa ga Amurka'', in ji shi.

    ''Gwamnatin Iran ta kashe ƴan Isra'ila da Amurkawa masu yawa, don haka bai kamata a bar wannan gwamnati ta malaki makamin nukiliya ba'', in Netanyahu.

    Yana mai cewa harin da suka kai zai bai wa Iraniyawa damar ƙwace gwamnatinsu da hannunsu.

  4. Trump ya buƙaci Iraniyawa su ƙwace gwamnatin ƙasar

    ..

    Asalin hoton, ..

    Shugaban Amurka Donald Trump ya buƙaci Iraniyawa su yi amfani da manyan hare-haren Amurka da Isra'ola wajen kifar da gwamnatin ƙasar.

    Cikin wani jawabi da ya yi ta bidiyo, Mista Trump ya ce ''Idan muka gama namu, ku kuma ku ƙwace gwamnatin, taku ce, ina ganin wannan ce damar da kuka samu ta yin hakan''.

    Ya kuma faɗa wa dakarun sojin Iran cewa za a ba su ''kariya'' idan suka amince su ajiya makamansu, ko kuma su ''fuskanci mutuwa''.

    A farkon watan Janairu ne Trump ya yi barazanar kai harin bom kan Iran saboda yadda jami'anm tsaron ƙasdar ke far wa masu zanga-zangar adawa da gwamnati, wadda ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta ce an kashe mutum 6,480.

  5. Iran ta ƙaddamar da hara-haren ramuwar gayya

    hari

    Iran ta ƙaddamar da hare-haren ramuwar gayya game da hare-haren da Isra'ila da Amurka suka kai mata da safiyar yau.

    Cikin wata sanarwa da rundunar sojin Isra'ila, IDF ta fitar, ta tabbatar da gano makamai masu linzami da Iran ta harba cikin Isra'ila, amma tana ƙoƙarin ganin ta kakkaɓo su.

    Haka ma Qatar ta tabbatar da cewa Iran ta kai hari kan wasu sansanonin sojin Amurka da ke ƙasaer, kodayake ta ce an kakkaɓo hare-haren.

    Ita ma ƙasar Bahrain ta tabbatar da kai hari kan sansanonin sojin ruwan Amurka da ke ƙasar, kodayake ba ta alaƙanta harin da kowace ƙasa ba.

  6. Mun gaji da batun yarjejeniya - Trump

    Trump

    Asalin hoton, ..

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Amurka ta gaji da batun yarjejeniyar nukiliyar Iran.

    Cikin wani bidiyon minti takwas da ya fitar a shafinsa na sada zumunta, shugaban na Amurka ya tabbatar da hannun AMurka a harin Iran.

    Ya tabbatar da cewa Amurka ta ƙaddamar da ''babban faɗa'' da Iran.

    ya ƙara da cewa ''Za mu wargaza makamanta masu linzami tare da lalata kamfanin ƙera makamanta da ke ƙarƙashin ƙasa...''

  7. Biranen Iran biyar da hare-haren suka faɗa

    Kamfanin dillancin labaran Iran na Fars ya bayar da rahoton birane biyar da aka samu faɗawar hare-hare a cikinsu.

    Biranen sun haɗa da Isfahan da Qom da Karaj da Kermanshah da kuma babban birnin ƙasar Tehran

    biranen Iran
  8. Hotunan yadda yahaƙi ke tashi a Iran bayan harin Isra'ila da Amurka

    Hoto

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Da safiyar yau Asabar en aka ji ƙarar abubuwan fashewa a birnin Tehran
    Iran
    Bayanan hoto, Tuni Iran ta rufe sararin samaniyarta
    Hoto

    Asalin hoton, Reuters

  9. Isra'ila da Iran sun rufe sararin samaniyarsu

    Isra'ila ta sanar da rufe sararin samniyartya bayan harin da haɗa gwiwa da Amurka suka kai wa Iran da safiyar yau Asabar, a cewar kafofin yaɗa labaran ƙasar.

    Can a Iran kamfanin dillancin labarai na Tasnim mai alaƙa da dakarun juyin juya halin ƙasar, ya bayar da rahoton cewar Iran ta rufe sararin samaniyarta.

    Ana sa Iran za ta ƙaddamar da harin ramuwar gayya kan Isr'ila da sansanonin sojin AMurka da ke gabas ta tsakiya.

  10. Amurka da Isra'ila sun ƙaddamar da hare-hare kan Iran

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce an ji ƙarar manyan abubuwan fashewar uku a birnin Tehran.

    Kamfanin dillancin labarai na Fars ya ce ya samu rahatonnin faɗawa makamai masu linzami a babban birnin Iran.

    Kafofin yaɗa labaran Amurka da na Isra'ila sun ce Amurka da Isra'ila ne suka haɗa gwiwa wajen ƙaddamar da harin.

    Dama dai Amurka ta jima tana barazanar far wa Iran da yaƙi saboda shirinta na nukiliya.

    A makon da ya gabata Shugaba Trump na Amurka ya bai wa ƙasar wa'adin kwana 10, don ta cimma yarjejeniya ko ta ɗauki matakin soji a kanta.