INEC ta sanya ranar zaɓukan cike gurbi a Kano, Gombe, Bauchi da Delta

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar zaɓe ta Najeriya, INEC, ta sanya ranar 19 ga watan Satumba domin gudanar da zaɓukan cike gurbi guda biyar a jihohin Gombe, Kano, Bauchi da Delta.
Sakataren yaɗa labarai na shugaban INEC, Tunde Oketola, ne ya bayyana wa kamfanin dillancin labaran Najeriya, NAN, cewa zaɓukan sun ƙunshina kujerar majalisar wakilai ta tarayya guda ɗaya da kuma kujerun majalisun jihohi huɗu.
Ya ce za a gudanar da zaɓen kujerar majalisar wakilai ta tarayya a mazabar Gombe/Kwami/Funakaye ta jihar Gombe.
Zaɓukan kujerun majalisar jihohin kuma za su gudana a mazabar Disina da Sakwa a jihar Bauchi, sannan Udu a jihar Delta da Dawakin Kudu a jihar Kano.



















