Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin kisa da babbar kotu ta yanke a kan Abdulmalik Tanko, wanda aka samu da laifin sacewa tare da kashe ƙaramar yarinya Hanifa Abubakar.
Hukuncin ya biyo bayan shari’ar da ta ja hankalin al’umma baki, inda kotu ta same shi da laifin aikata kisan.
Wannan mataki, a cewar gwamnatin jihar Kano, wata babbar nasara ce domin tabbatar da adalci, wanda ke ƙarfafa gwiwar mutane domin su ƙara al’umma da ɓangaren, tare da tabbatar da cewa waɗanda suka aikata manyan laifuka, musamman waɗanda suka shafi kisan yara, ba za su tafi a banza ba.
Sanarwar tabbatar da hukuncin na ɗauke ne a wani rubutu da babban lauyan jihar kuma kwamishinan shari’a, Abdulkarim Kabiru Maude ya sanar, inda ya yaba da hukuncin yana mai cewa hakan ya nuna ƙarfin doka da jajircewar ɓangaren shari’a wajen kare rayuka, musamman na yara da sauran masu rauni a cikin al’umma.
Ya ce "Wannan hukunci ya sake jaddada cewa doka tana aiki ba tare da tsoro ko nuna son kai ba."
Maude ya kuma yaba wa Barrista Lamido Abba Sorondinki, lauyan gwamnati a ma’aikatar shari’a ta jihar bisa abin da ya kira jajircewa da ƙwarewarsa wajen bin diddigin shari’ar har zuwa matakin tabbatar da hukuncin.
A watan Disambar 2021 ne Abdulmalik Tanko ya sace Hanifa inda daga bisani ya kashe ta lamarin da ya girgiza al’umma a Kano da ma ƙasar baki ɗaya.
An kama Abdulmalik Tanko a watan Janairun 2022 bayan binciken jami’an tsaro, lamarin da ya kai ga gurfanar da shi a gaban kotu da kuma yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya wanda yanzu kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar.