Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Labaran wasannin BBC Hausa kai-tsaye 4-10 Janairu, 2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa kai-tsaye daga ranar 4 zuwa 10 ga watan Janairu, 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Muhammed Abdu, Haruna Kakangi

  1. Saka ya tsawaita zaman shi a Arsenal

    Bukayo Saka ya amince da tsawaita zaman shi a kungiyar Arsenal ta hanyar sanya hannu kan kwantaragi na dogon wa’adi.

    Mun fahimci cewa sabon kwantaragin zai sanya Saka, mai shekara 24 ya zama dan wasa da ya fi kowane daukan albashi mai tsoka.

    Wannan kwantaragi na daga cikin dabarun Arsenal na baya-bayan nan domin rike manyan ‘yanwasanta, a kokarin ganin ta lashe kofi.

    William Saliba, da Gabriel Magalhaes, da Ethan Nwaneri da kuma Myles Lewis-Skelly dukkaninsu sun sanya hannu kan sabbin kwantaragi masu dogon wa’adi a baya-bayan nan.

    Saka, mai buga wa Ingila wasa ya zama babban ginshiki a Arsenal tun bayan fara wasa a shekarar 2018, bayan ya samu horo a tawagar yara ta kungiyar.

    A kakar wasa da ta gabata Saka ya ci wa Arsenal kwallo 12, sannan ya taimaka aka zura 13 a wasa 37 da ya buga duk da cewa ya yi fama da rauni na tsawon watanni uku.

    Ya zama kyaftin din kungiyar karon farko a kakar wasa ta 2023-24, inda ya kammala kakar a matsayin dan wasan da ya fi yawan kwallaye bayan ya ci kwallo 20.

  2. Man City ta kammala sayen Semanyo daga Bournemouth

    Man City ta kammala sayen ɗan wasan gefen Bournemouth - Antoine Semenyo ka fam miliya 65.

    Ƙungiyar ta Ettihad ta doke manyan ƙungiyoyin Premier irin su Manchester United da Liverpool da Tottenham da kuma Chelsea wajen ɗaukar ɗan wasan mai shekara 26.

    Semenyo - wanda aka haifa tare da tasowa a Ingila -na wakilatar Ghana a matakin ƙasa, kasancewa ƙasar mahaifinsa.

    Tauraron ɗan wasan ya fara haskawa tun bayan komawarsa Bournemouth data Bristol City a 2023 kan fam miliyan 10.

    Man City ta ɗauki ɗan wasan ne a ƙoƙarinta ta gyara tawagar ƙungiyar da ke mataki na biyu da tazarar maki shida a teburin Premier.

  3. Za a buga wasan El-clasico na farko a 2026 ranar Lahadi

    Za a yi gumurzun wasan hamayyar ƙungiyoyin Sifaniya da ake yi wa laƙabi da El-Clasico tsakanin manyan ƙungiyoyin ƙasar biyu, Real Madrid da Barcelona ranar Lahadi mai zuwa a ƙasar Saudiyya.

    Ƙungiyoyin za su kara ne a wasan ƙarshe na Spanish Super Cup a filin wasa na King Abdullah da ke birnin Riyadh.

    Madrid ta kai matakin ne bayan doke abokiyar hamayyarta a birnin Madrid, Atletico Madrid da ci 2-1 a ranar Alhamis da maraice.

    Yayin da ita kuwa Barcelona ta kai matakain bayan doke Athletic Bilbao 5-0 a ranar Laraba.

    Wannan ce karawar hamayya ta farko tsakanin manyan ƙungiyoyin na Sifaniya a shekarar 2026.

  4. An ga kocin Tottenham na shan shayi a kofi mai tambarin Arsenal

    Mai horas da ƙungiyar Tottenham, Thomas Frank na shan kakkausar suka sanadiyyar kofin da aka hango shi riƙe da shi.

    Kofin da ya riƙe yana shan wani abu da babu tabbas ko gahawa ne ko shayi ko madara – ko ma dai mene ne, ya yi matuƙar janyo hankalin kafafen yaɗa labari.

    Gabanin karawar Tottenham da Bournemouth a ranar Laraba, an ɗauki hoton mai horas da Tottenham din rike da kofi mai tambarin ƙungiyar Arsenal ɓaro-ɓaro yana tattaki a filin wasa na Vitality Stadium.

    Wannan babban abin mamaki ne ganin cewa shi ne mai horas da ƙungiyar da ba ta taɓa yin ga-maciji da ƙungiyar Arsenal ba.

    Bugu da ƙari rashin taɓuka abin kirkin kociyan na Tottenham ya ƙara iza wutar nuna rashin jin daɗi kan halayyar sa a tsakanin magoya bayan ƙungiyar.

    BBC ta gane cewa wani ma’aikaci a filin wasan ne ya bai wa Frank gahawa a cikin kofin wanda ƴan Arsenal suka bari a filin wasan bayan karawar da suka yi da Bournemouth kwana huɗu kafin ranar.

    Akwai yiwuwar cewa daga Frank ɗin har ma‘aikacin da ya ba shi gahawar ba su lura da tambarin Arsenal a jikin kofin ba har sai da mutane suka riga suka gani.

  5. "Muna shan wahala" - Guardiola

    Ƙungiyar Manchester City ta lashe gasar Premier League guda shida a kaka 8 da Pep Guardiola ya horas da ƴanwasanta, amma yadda ƙungiyar ta rasa maki shida a wasa uku da suka gabata ya sa yunƙurin lashe kofin na bakwai a zamanin Guardiola ya fara lilo.

    Da yake jawabi game da wasannin, Pep ya ce, "mun gaza samun nasara a wasa guda uku a jere wato canjaras da Sunderland da Chelsea da Brighton. Gaskiya lashe gasar zan zai mana wahala, amma za mu ci gaba da ƙoƙarin abin da za mu iya," in ji shi.

    Yawan yin canjaras na dusashe yiwuwar cin Premier ga City

    Da a ce City ta samu nasara a wasannin guda uku da ta yi canjaras, da yanzu ita ce a saman teburi, kuma da ta ƙara ɗaga wa Arsenal hankali a wasanta na gida da Liverpool a yau.

    Yanzu dai Gunners ta ba City tazarar maki biyar, kuma za ta iya ƙara faɗaɗa tazarar zuwa maki takwas idan ta doke Liverpool a yau.

  6. Ko Arsenal za ta iya bayar da tazarar maki 8 a wasan yau?

    Wasannin gasar Premier League dai tana ƙara zafi, musamman bayan fara wasannin watan Janairu, inda ƙungiyoyi huɗu na saman teburin suke bin juna kusa da kusa.

    Sai dai kallo ya koma filin wasa na Emirates ne a yau, inda Arsenal wadda ke saman teburi za ta fafata da mai riƙe da kambun gasar wato Liverpool.

    Idan Arsenal ta doke Liverpool a wasan na yau, ƙungiyar wadda Mike Artete ke horaswa za ta ƙara faɗaɗa tazarar da ke tsakaninta da ƙungiyoyi biyu da ke biye mata da maki 8.

    Ƙungiyoyi biyu da ke biye mata su ne Manchester City da Aston Villa da kowannensu ke da 43, bayan dukansu sun yi canjaras a wasannin da suka buga a daren ranar Laraba.

  7. Ɗan wasan Brazil, Neymar, ya tsawaita kwantiraginsa da Santos har zuwa ƙarshen kakar 2026, yayin da yake ƙoƙarin ganin an gayyace shi gasar cin kofin duniya.

    Ɗan wasan mai shekaru 33, wanda ya koma ƙungiyar da ya fara yiwa tamaula tun yana matashi, bai buga wa Brazil wasanni ba, saboda fama da jinya.

    Tsohon ɗan wasan Barcelona da Paris St-Germain ya na buga wasanni duk da raunin da yake ɗauke da shi domin taimaka wa Santos wadda ba ta faɗi ba daga babbar gasar Brazil a kakar da ta wuce, inda ya zura ƙwallaye biyar a wasa biyar na ƙarshe.

    Daga bisani an yi masa tiyata a gwiwar ƙafarsa ta hagu, don ya samu shiga cikin tsare-tsaren kocin Brazil, Carlo Ancelotti, a wannan bazarar.

    Ancelotti ya sanar a watan Oktoba cewa dole ne Neymar — wanda shi ne dan wasan da ya fi kowa zura kwallaye a tarihin Brazil da guda 79 a raga — ya kasance cikin koshin lafiya kuma kan ganiya kafin a sake kiransa.

    Neymar ya shafe wata 12 ba tare da buga wasa ba bayan jijiyar gwiwa a watan Oktoban 2023.

    An shirya zai koma cikin tawagar kasa a bara bayan wata 17 na rashin buga wasa, amma an tilasta masa janyewa daga tawagar sakamakon raunin da ya ji.

    Brazil za ta kara da Scotland da Morocco da Haiti a rukuni na uku a gasar cin kofin duniya, wadda za ta fara wasa a ranar 11 ga watan Yuni a wasanin da za a yi haɗaka a Amurka da Canada da kuma Mexico.

  8. , Daga Jaridu

    Newcastle United za ta yi gogayya da Tottenham idan ta koma wurin kungiyar Wolves a kokarin da take yi domin siyan dan wasan NorwayJorgen Strand Larsen mai shekara 25. (ChronicleLive)

    Tottenham za ta sayi wani sabon dan wasan gaba a watan nan na Janairu saboda raunin da dan wasan Ghana Mohammed Kudus, mai shekara 25 ya ji , ya yi muni fiye da yadda suka yi tunani tun farko. (Telegraph)

    Darektan kungiyar Roma, Ricky Massara ya ce halin da ake ciki game da duk wani yunkuri na siyan dan wasan gaban Manchester United Joshua Zirkzee, mai shekara 24, ya sauya saboda korar da aka yi wa kocin kungiyar ta Old Trafford, Ruben Amorim (Sky Sports)

    Fatan da Juventus take da shi na siyan dan wasan Italiya Federico Chiesa, mai shekara 28, daga Liverpool ya dogara ne kan ko dan wasan Masar Mohamed Salah, mai shekara 33, zai ci gaba da taka leda a Anfield. (La Gazzetta dello Sport)

    Ita ma Napoli na son Chiesa sai dai Liverpool ba ta sami wani tayi a hukumance ba daga wata kungiya ba kuma abu ne mai wuya ta sayar da shi a watan Janairu. (Sky Sports News)

  9. Za a bayar da ladan Dalar Amurka miliyan 75 a Australia Open, Australian Open

    An ƙara kuɗin kyautar lashe gasar Australian Open ta bana da kashi 16 cikin 100 zuwa dalar Amurka miliyan 111.5, wanda ya sa ya zama mafi girman kuɗin lada a tarihin gasar, kamar yadda masu shirya gasar suka sanar a ranar Talata.

    Duk namji da macen da za ta lashe kofin bana za su karɓi kowannensu dalar Amurka miliyan 4.15, wanda ya haura dala miliyan 3.5 miliyan da Jannik Sinner da Madison Keys suka samu a bara.

  10. Yadda aka samu takwas da za su kara a ƴan takwas a Afcon, Afcon Morocco 2025/26

    An kammala wasannin zagayen ƴan 16 a gasar cin kofin Afirka da ake yi a Moroko.

    Tawagogin ƙasashe sun yi fafatawa mai zafi, an nuna bajinta da kuma ƙwarewa.

    Yanzu dai daga cikin ƴan 16, ƙasashe takwas sun fice daga gasar yayin da takwas suka tsallaka zuwa zagayen kwata-fainal.

    Za a fara gwabzawa a zagayen na kwata-fainal ne ranar Juma'a, 9 ga watan Janairun 2026.

    Mun yi duba kan ƙasashe da za su fafata da kuma abin da ake sa ran gani.

  11. Ten Hag zai koma aiki a tsohuwar ƙungiyarsa, FC Twente, FC Twente

    Tsohon kociyan Manchester United, Erik ten Hag zai sake komawa tsohuwar kungiyarsa FC Twentae a matakin daraktan tsare tsare daga farkon kakar badi - kamar yadda yadda aka sanar ranar Laraba.

    Ya kuma sa hannun kan yarjejeniyar zuwa karshen kakar 2028 a kungiyar da ya fara taka leda daga 1989 zuwa 2002.

    Kenan mai shekara 55 zai fara aiki daga 1 ga watan Fabrairu, zai maye gurbin Jan Steuer, wanda ya ajiye aikin.

  12. Jones ta kai kwata fainal a ATP a Aucland, Ƙwalon tennis

    Ƴar Burtaniya, Francesca Jones ta kai zagayen kwata fainals bayan doke Sinja Kraus a ATP a Aucland.

    Tana buga wasannin ne domin shirin buga gasar Australian Open da za a fara 18 ga watan nan na Janairu.

  13. An samu tawaga takwas da za ta buga kwata fainals a Afcon, Afcon Morocco 2025/26

    Ranar Talata aka kammala wasannin zagaye na biyu a babbar gasar tamaula ta Afirka da ake yi a Morocco.

    Tawagar da ta kai zagaye na uku a babbar gasar tamaula ta Afirka ta hada da mai masaukin baki Morocco da Kamaru da Mali da Senegal da Masar da Aljeriya da Najeriya da kuma mai rike da kofin Ivory Coast.

    Kuma daga cikinsu Mali ce ba ta taba lashe Afcon ba, amma a tsakaninsu suna da kofi 22.

    Cikin takwas da za su buga kwata fainal biyar daga ciki za su wakilci Afirka a gasar kofin duniya a bana da ya hada da Morocco da Senegal da Masar da Aljeriya da kuma Ivory Coast.

    Zuwa wannan matakin an buga wasa 44 da cin kwallo 109, Brahim Diaz na Morocco ne kan gaba mai hudu a raga.

    Sai a ranar Juma'a zuwa Asabar za a buga wasannin kwata fainals.

    Za a kara tsakanin Mali da Senegal da na Kamaru da Morocco.

    Sannan Najeriya da Aljeriya da na Masar da Ivory Coast.

  14. , Daga Jaridu

    Dan wasa mai kai hari na Poland Robert Lewandowski ba ya son ya bar Barcelona a watan Janairu duk da cewa akwai kungiyoyi da dama da ke zawarcin dan wasan mai shekara 37. (Sky Sports)

    Bayern Munich ta tsawaita kwantaragin dan wasan bayan Faransa Dayot Upamecano, mai shekara 27 wanda wa'adinsa a kungiyar zai kare a bazara. (Sky Sports)

    AC Milan na zawarcin dan wasan Bayern Munich Kim Min-jae, mai shekara 29, sai dai za ta nemi taimakon kungiyar ta Jamus ta bada gudummawa kan albashin dan wasan kasar Koriya ta Kudu domin su iya kulla yarjejeniya. (La Gazzetta dello Sport)

    Dan wasa mai kai hari na Real Madrid, Endrick mai shekara 19 wanda ya je Lyon a matsayin aro ya ce kocin Brazil Carlo Ancelotti ne ya ba shi shawarar barin kungiyar ta Sifaniya domin ya kara samun kwarewa wajen buga tamaula . (Goal)

    Yarjejeniyar da Leicester City ta gabatar wa dan wasa mai kai hari Michail Antonio, kuma tsohon dan wasan West Ham, ta wargaje sakamakon raunin da ya ji. Dan wasan Jamaica mai shekara 35 bai buga wasa ba tun bayan hadarin motar da ya yi a watan Disambar 2024, amma yana tattaunawa kan kwantaragin gajeren zango (Talksport)

    Dan wasan Koriya ta Kudu Yang Min-hyeok, mai shekara 19, na gab da komawa South Coventry City a matsayin aro daga Tottenham. (Fabrizio Romano)

  15. Wasannin Premier League mako na 21 da za a buga, Premier League

    Ranar Laraba, 07 ga watan Janairu

    • Bournemouth da Tottenham
    • Brentford da Sunderland
    • Crystal Palace da Aston Villa
    • Everton da Wolves
    • Fulham da Chelsea
    • Manchester City da Brighton
    • Burnley da Manchester United (20:15)
    • Newcastle United da Leeds United (20:15)

    Ranar Alhamis, 08 ga watan Janairu

    • Arsenal da Liverpool (20:00)
  16. Watakila a bai wa Carrick da Solskjaer aikin riƙon ƙwarya a United, Manchester United

    Michael Carrick da Ole Gunnar Solskjaer suna gaba-gaba a matsayin ƴan takarar neman kocin riƙon ƙwarya a Manchester United har zuwa ƙarshen kakar bana.

    Tsoffin ƴan wasan United biyu, waɗanda sun taɓa horar da ƙungiyar a baya, ana sa ran za su tattaunawar kai tsaye da shugabancin ƙungiyar Old Trafford.

    Watakila su yi aikin tare, domin Carrick ya taka muhimmiyar rawa a cikin masu horarwa a lokacin da Solskjaer ya maye gurbin Jose Mourinho a Old Trafford a 2018.

    Darren Fletcher, kocin matasan United ƴan kasa da shekara 18, shi ne aikin riƙon ƙwarya, kuma shi ne zai ja ragamar ƙungiyar a wasan Premier League da Burnley ranar Laraba.

    Ana kuma cewa Ruud van Nistelrooy, tsohon ɗan wasan gaba na United, zai kasance shima a cikin ƴan takara.

    An koro Amorim a ranar Litinin bayan watanni 14 yana horar da United cikin ɗan karen kalubale.

    United na shirin naɗa sabon koci na dindindin da zai maye gurbin Amorim da zarar an kammala kakar bana.

    Solskjaer ya fara jagorantar ƙungiyar a irin wannan yanayi ne lokacin da United ta sallami Mourinho a 2018, daga bisani kuma aka ba shi cikakken aikin horarwa na tsawon shekaru uku kafin a sallame shi a watan Nuwamba 2021.

    Carrick daga baya ya jagoranci ƙungiyar wasa uku a matsayin kocin wucin gadi bayan sallamar Solskjaer, kafin ya bar United a watan Disamba 2021.

    Tsohon ɗan wasan tsakiyar Ingila ba shi da wata ƙungiyar da yake horarwa tun bayan da aka sallame shi daga ƙungiyar Championship, Middlesbrough, a watan Yuni da ya gabata bayan shekaru biyu da rabi yana jagoranci.

    An sallami Solskjaer daga ƙungiyarsa a Turkiyya, Besiktas, a watan Agusta.

    Kocin Crystal Palace, Oliver Glasner, da tsohon kocin Brighton, Roberto de Zerbi — wanda yanzu yake horar da Marseille — an fahimci suna cikin ƴan takara.

  17. Kokarin da Burkina Faso ke yi a Afcon a tarihi, Afcon Morocco 2025/26

    • Ta kawo wannan gurbin ne, bayan nasara a kan Equatorial Guinea da Sudan, sannan Algeria ta doke ta.
    • Ta haura matakin zagaye na biyu a 2021, amma aka yi waje da ita a irin wannan matakin a 2013.
    • A wasan farko a zagayen ƴan 16 a 2021 ta fara yin 1-1 da Gabon har da karin lokaci daga baya ta yi nasara 7-6 a bugun fenariti.
    • Sai ta yi rashin nasara 2-1 a hannun Mali a zagayen ƴan 16 a 2023.
    • Idan ta yi nasara za ta kara a karo na biyar a kwata fainal (1998, 2013, 2017 da kuma 2021).
    • Dukkan wasan da ta buga zagayen ziri ɗaya kwale ba ta tashi 0-0
    • Issoufou Dayo da Hervé Koffi da Arsène Kouassi da kuma Edmond Tapsoba sun buga wa Burkina Faso dukkan karawa uku ta cikin rukuni a Afcon a Morocco.
  18. Bajintar da Ivory Coast ke yi a gasar kofin Afirka, Afcon Morocco 2025/26

    • Ta kawo wannan matakin bayan nasara a kan Mozambique da Gabon da yin canjaras da Kamaru.
    • Karo na huɗu kenan a baya-bayan nan da za ta fafata a zagaye na biyu - a baya ta kai wannan gurbin a 2019 da 2023 daga baya aka yi waje da ita a 2021.
    • Wadda take rike da kofin ba ta yin nasara a zagayen ƴan 16 a Afcon tun bayan Masar da ta yi wannan bajintar a 2010.
    • Tun daga 2010, duk wadda take rike da Afcon ba ta iya zuwa matakin kwata fainal tun daga Zambia (2013) da Ivory Coast (2017) da Kamaru (2019) da Algeria (2021) da kuma Senegal (2023).
    • A matakin mai rike da Afcon, karo na biyu kenan da Ivory Coast ke haura matakin karawar cikin rukuni, bayan 2017 da take da Afcon.
    • Idan har ta yi nasara za ta kai kwata fainal a Afcon karo na 12 jimilla (1992, 1994, 1998, 2006, 2008, 2010, 2012, 2013, 2015, 2019 da kuma 2023).
    • Amad Diallo ya ci ƙwallo biyu a Morocco, watakila ya zama ɗan kasar na farko da zai zura uku ko fiye da haka a gasa, bayan kwazon Didier Drogba a 2012.
    • Ba a doke koci, Emerse Faé ba a wasannin Afcon, tun bayan da aka bashi aikin, ya ja ragamar wasa bakawi da cin biyar da canjaras biyu.
  19. Super Eagles za ta kara tsakanin Aljeriya ko Dr Congo, Afcon Morocco 2025/26

    Tawagar Najeriya ta kai kwata fainal a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake yi a Morocco ranar Litinin.

    Ta kuma kai zagayen gaba, sakamakon doke Mozambique 4-0, ita ce ta farko da ta ci ƙwallo huɗu a wasannin bana, kuma tana da 12 yayin da huɗu suka shiga ragarta.

    Za ta kara a zagayen ƴan takwas da duk wadda ta yi nasara tsakanin Aljeriya ko kuma Jamhuriyar Congo.

  20. Evans zai koma United domin ya taimakawa Fletcher, Manchester United

    Jonny Evans zai sake komawa Manchester United domin ya taimakawa kociyan rikon kwarya, Darren Fletcher gudanar da aiki.

    Ita kuwa West Bromwich Albion na neman sabon kociya, bayan da ta kori Ryan Mason.