A wani mataki na nuna fushinsa, Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ƙasarsa ba ta buƙatar taimakon Birtaniya a yaƙin da take yi a Iran.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Shugaba Trump ya ce Amurka ba ta buƙatar manyan jiragen dakon kaya na Birtaniya biyu a Gabas ta Tsakiya.
"Birtaniya, ɗaya daga cikin manyan ƙawayenmu, watakila ma babba cikin ƙawayen namu, a yanzu na nuna shakku kan tura manyan jiragensu biyu zuwa Gabas ta Tsakiya. Amma ba komai'', kamar yadda ya wallafa.
''Amma firministan Birtnaiya ka sanin mu yanzu ma ba ma buƙatarsu - Amma za mu riƙa tuna wannan. Mu ba ma son ma mutane su shigar mana yaƙi bayan mun riga mnun yi nasara''.
Wanna na zuwa ne bayan Staemer ya ƙi amincewa Amurka ta yi amfani da sansanonin sojin Birtaniya a yankin Gabas ta Tsakiya don kai wa Iran hare-hae.
Daga baya Trump ya ce ''Ba ya son taimaka mana''.
“Ban taɓa tsammanin haka ba, ban taɓa tsammanin Birtaniya za ta yi mana haka ba,'' kamar yadda ya shaida wa Jaridar The Sun.
Gwamnatin Birtaniya dai ba ta shiga yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran ba, sannan ba ta yi alƙawarin shiga ba.