Firaministan Birtaniya ya isa UAE don tattaunawa kan yaƙin Iran
Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya isa ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a ci gaba da ziyararsa da yake yi a Gabas ta Tsakiya domin tattaunawa kan rikicin Iran.
Ziyarar ta zo ne a lokacin da tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran ke fuskantar ƙalubale, yayin da Iran ta bayyana cewa ci gaba da hare‑haren Isra’ila a Labanon wani “babban keta yarjejeniyar” ne.
A baya, Starmer ya gana da Yarima Mohammed bin Salman na Saudiyya a birnin Jeddah, kuma ana sa ran zai gana da Shugaban UAE, Sheikh Mohammed bin Zayed Al Nahyan don ci gaba da tattaunawa kan matsalolin tsaro da zaman lafiya a yankin. .