Iran da Saudiyya sun tattauna ta waya a karon farko tun bayan fara yaƙi
Ministan harkokin Wajen Saudiyya, Prince Faisal bin Farhan Al Saud, ya tattaunawa ta waya da takwaransa na Iran, Abbas Araqchi, a karon farko tun bayan ɓarkewar yaƙi da hare‑haren Iran a yankin Gabas ta Tsakiya.
Wannan shi ne mataki na farko na hulɗa kai tsaye tsakanin ƙasashe biyu a cikin wannan rikici.
Ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya ta bayyana a shafin ta na X cewa ministocin biyu sun tattauna kan sabbin abubuwan da suka faru a yankin, tare da bincikar hanyoyin rage tashin hankali don dawo da tsaro da kwanciyar hankali a yankin








