Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na 20 ga watan Maris 2025

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Nabeela Mukhtar Uba da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Rasha da Ukraine za su tattauna a mako mai zuwa

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce jami'an Ukraine za su tattauna da takwarorin aikinsu na Amurka a ƙasar Saudiyya a ranar Litinin mai zuwa, kuma wannan na zuwa ne bayan Rasha ta tabbatar cewa wakilanta za su tattauna da jami'an Amurka a ranar ta Litinin.

    Jerin tattaunawar ta baya-bayan nan na zuwa ne yayin da Amurka ke ƙoƙarin samar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ƙasashen biyu bayan fiye da shekara uku ana gwabza yaƙi.

    Shugaban Ukraine ya ce ya zama wajibi Rasha ta daina "gindaya sharuɗɗa marasa tushe waɗanda ke tsawaita yaƙin."

    Shugaban Rasha Vladimir Putin na neman a yanke duk wani tallafin makamai da ƙasashe ke bai wa Ukraine.

    Haka nan Zelensky ya yi gargaɗin cewa yin watsi da batun shigar Ukraine ƙungiyar NATO - wata buƙata da Rasha ta gabatar - tamkar "bai wa Rasha garaɓasa ne".

  2. Babu ruwanmu na yarjejeniyar tsagaita wutar Kongo da aka cimma - M23

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Shugaban ƙungiyar ƴan tawayen M23 ya bayyana cewa babu wani nauyi da ya rataya a kan ƙungiyar kan martaba yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma tsakanin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo da Rwanda a ƙasar Qatar a farkon wannan mako.

    Corneille Nngaa ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa "matuƙar ba za ta warware mana matalarmu ba" abin da ya faru a Doha "babu ruwanmu da shi."

    Ya kuma yi watsi da wani tayin bayar da ma'adanai ga Amurka domin samar da tsaro.

    A ranar Laraba, mayaƙan M23 masu samun goyon bayan Rwanda suka karɓe iko da wani muhimmin birni mai arziƙin ma'adanai - wanda hakan ya ba su damar faɗaɗa ikonsu ta lardin North Kivu.

  3. Masu zanga-zanga sun bijire wa umarnin gwamnati a Turkiyya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Dandazon masu zanga-zanga sun bijire wa haramcin da aka sanya na duk wani gangami a birnin Istanbul na ƙasar Turkiyya, inda suke nuna goyon bayansu ga magajin garin birnin wanda ke tsare a hannun hukumomi.

    Ekrem Imamoglu - wanda shi ne jagoran ƴan'adawar ƙasar kuma mai ƙalubalantar shugaban ƙasar Receb Erdogan - an kama shi ne kwanaki kaɗan gabanin ranar da ake shirin bayyana shi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasar na shekarar 2028.

    Ana zargin shi da rashawa da kuma taimaka wa ƙungiyar ta'addanci.

    Shugaban jam'iyyar adawa Ozgur Ozel, ya zargi shugaba Erdogan da shakkar zaɓe, ya kuma shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa duk wani yunƙuri na haramta wa Mr Imamoglu yin takara zai ƙara ƙarfin goyon bayan da yake da shi ne.

  4. Yadda ake yin Sakwarar Gwaza da miyar Egusi

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo

    A filinmu na girke-girken Ramadan na yau, Sadiya Hashim Sabo wadda aka fi sani da Sadywise Kitchen za ta nuna muku yadda ake girka sakwarar gwaza da miyar egusi sai kuma abin sha na beetroot.

  5. Tinubu ya yaba wa majalisa bisa tabbatar da dokar ta-ɓaci a Rivers

    Tinubu

    Asalin hoton, Twittter/@officialABAT

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yaba wa majalisar dokoki bisa tabbatar da ayyana dokar ta-ɓacin da ya yi a jihar Rivers, inda ya ce ƴan majalisar sun yi ƙoƙari wajen ajiye bambancin siyasa tare da fitita matsalar tsaro.

    A wata sanarwa da kakakinsa, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce sun ɗauki matakin ne domin wanzar da zaman lafiya da magance rikicin siyasar da ya dabaibaye jihar na kusan wata 15.

    "Rikicin jihar Rivers ya yi riga ya yi ƙamari, har yake barazana ga kadadorin man fetur, kuma yake yunƙurin kawo tsaiko ga tattalin arziki da mayar da hannun agogo baya a ƙoƙarin da muke yi wajen daidaita ƙasar.

    "Matakin da kuka ɗauka a yau ya nuna cewa ƙasarmu za ta samu nasarori da ci gaba idan aka samu haɗin kai."

    Shugaba Tinubu ya ce dokar ta-ɓacin ta wata shida za ta ba shugaban riƙon damar saita al'amura ne a Rivers, tare da tabbatar da sulhu a tsakanin ɓangarorin da suke saɓani.

    Tinubu ya kuma yi godiya ga ƴa Najeriya bisa fahimtarsa da suka yi, sannan ya yi kira da dukkan masu ruwa da tsaki da su goya masa baya wajen mayar da zaman lafiya a jihar ta Rivers.

  6. Hukumar Nimet ta gargaɗi kan ɓullar cutar sanƙarau a Najeriya

    Nimet

    Asalin hoton, Google

    Hukumar kula da yanayi ta Najeriya Nimet ta yi gargaɗin cewa wasu jihohin arewacin ƙasar na ƙara fuskantar barazanar ɓarkewar cutar sanƙarau.

    Nimet a cikin sanarwar da ta wallafa a shafinta na X, ta ce jihohin Sokoto da Kebbi da Zamfara da Katsina da Kano da Jigawa da Bauchi da Yobe da Gombe da kuma Borno su ne suka fi fuskantar barazanar.

    Hukumar ta kuma ce alamomin cutar sanƙarau sun haɗa da zazzaɓi mai zafi da ciwon kai mai tsanani da riƙewar wuya da amai, sai rashin son kallon haske da ruɗewa da kuma ƙuraje.

    Nimet ta kuma ƙara da cewa ana iya kamuwa da cutar da hanyar mu'amula da masu ɗauke da cutar da kuma shiga cunkoso, inda ta buƙaci alumma su yi rigakafi su wanke hannu su kuma gujewa kusantar masu cutar su kuma rufe bakinsu da hanci.

    Hukumar ta kuma yi kira ga alumma da su yi gaggawan zuwa asibiti idan sun ji alamomin da aka bayyana.

    https://x.com/nimetnigeria/status/1902450582646091798?s=46&t=-fB6xkzT5uxT97yUerJAog

  7. Aƙalla ƴan Afirka ta kudu 70,000 suka nuna sha'awar neman mafaka a Amurka

    Africaners

    Asalin hoton, AFP

    Aƙalla ƴan Afirka ta Kudu 70,000 ne suka bayyana sha'awarsu ta komawa Amurka bayan gwamnatin Amurkar ta yi tayin sake tsugunar da mutane daga alummar fararen fata da ke zaune a ƙasar, a cewar wata ƙungiyar kasuwanci.

    Cibiyar kasuwanci ta Afirka ta Kudu da ke Amurka (Saccusa) ta ce dubun dubatar mutane ne suka yi rijista a shafinta na yanar gizo dmin neman ƙarin bayani.

    A wani umurnin shugaban ƙasa a watan Fabrairu, shugaba Donald Trump ya ce za a iya karɓar fararen fata da ke zaune a Afirka ta kudu - waɗanda da dama suka zo a ƙarni na 17 - a matsayin ƴan gudun hijira ganin cewa sun kasance ''mutanen da aka yi wa wariyar launin fata da rashin adalci''.

    Alaƙa tsakanin Amurka da Afirka ta Kudu na ƙara tsami tun bayan lokacin da Trump ya hau mulki a watan Janairu.

  8. Hamas ta harba rokoki uku zuwa Isra'ila

    Hamas

    Asalin hoton, Reuters

    Hamas ta ce ta harba rokoki uku zuwa Isra'ila daga Gaza.

    Sai dai Isra'ilar ta ce ta kakkaɓo ɗaya daga ciki sannan babu wanda ya jikkata.

    A wani labarin, rundunar sojin Isra'ila ta gargadi Falasɗinawa da su kaucewa babbar hanyar shiga Gaza.

    Rundunar ta ce ta jibge dakarunta kan babbar hanyar da ta haɗa arewaci da kudancin Gaza.

    Kafar watsa labaran Isra'ila ta ruwaito cewa wanann wani sabon umarni ne ga Falasɗianwa da su janye daga arewaci zuwa kudancin Gaza.

    Ma'aikatar lafiya ta Gaza da Hamas ke jagoranta ta ce aƙalla Falasɗinawa 600 aka kashe cikin hare-haren da Isra'ila ta kai Gaza cikin kwanaki uku.

  9. Vice Admiral Ibok-Ete ya yi ganawar sirri da manyan jami'an tsaron Rivers

    Rivers

    Asalin hoton, RSGH MEDIA

    Mai riƙon muƙamin gwamnan jihar Rivers, Vice Admiral Ibok Ete Ibas mai ritaya ya yi wata ganawar sirri da manyan jami'an tsaro da tawagar gwamnatin tarayya da jami'an gwamnatin jihar a Fadar gwamnatin Rivers da ke Portharcourt.

    An samu halartar shugaban ma'aikata da manyan sakatarori da jami'an tsaro a taron a ofishin gwamnan Rivers.

    Ibas ya yi alkawarin yi wa manema labarai jawabi da zarar ya saurari ƙarin bayani daga jami'an gwamnatin jihar da kuma manyan kwamandojin tsaro.

    Ibas ya isa fadar ta Rivers ne tare da wasu manyan sojoji da wakilin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro.

    Rivers

    Asalin hoton, RSGH MEDIA

    Rivers

    Asalin hoton, RSGH MEDIA

    Rivers

    Asalin hoton, RSGH MEDIA

  10. Alamomin gane daren Lailatul Qadr

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo

    Daren Lailatul Qadr dare ne mafi girma da ɗaukaka ga musulmi. A daren Lailatul Qadr cikin kwanakin 10 ta ƙarshen wata Ramadan aka saukar da Al Qur’ani mai tsarki.

    Musulmi kan fatan dacewa da daren wanda Allah Ya ce ya fi wata 1,000 daraja.

    Ɗaya daga cikin manyan malaman addinin Islama a jihar Kano arewacin Najeriya Sheikh Aminu Daurawa ya yi bayani game da daren da kuma alamomin Lailatul Qadr.

  11. M23 sun ƙwace muhimmin gari mai arzikin ma'adanai a Kivu

    A watan da ya gabata ne, M23 ta ƙwace babban birni mai arzikin ma'adanai a gabashin Congo

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, A watan da ya gabata ne, M23 ta ƙwace babban birni mai arzikin ma'adanai a gabashin Congo

    Yan tawayen M23 sun ƙwace iko da wani muhimmin gari da ake haƙar ma'adanai a arewacin lardin Kivu, yayin da ƴan tawayen ke ci gaba da faɗaɗa hare-hare a gabashin Jamhuriyar Dimokradiyyar Kongo.

    Majiyar jami'an tsaro ta ce ƴan tawayen da ke samun goyon bayan Rwanda sun shiga garin Walikale a jiya Laraba.

    Garin yana kusa da ɗaya daga cikin yankin da ake haƙo wani ma'adanin ƙasa mai mahimmanci a duniya.

    Ƙwace iko da Walikale na zuwa ne duk da kiraye-kirayen tsagaita wuta da shugabannin ƙasashen Kongo da Rwanda suka yi a ranar Talata bayan tattaunawarsu ta farko.

  12. Hare-haren Isra'ila sun kashe aƙalla Falasɗinawa 85

    Isra'ila ta zafafa kai hare-hare a Gaza ranar Talata

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Isra'ila ta zafafa kai hare-hare a Gaza ranar Talata

    Aƙalla Falasɗinawa 85 aka kashe a hare-haren cikin dare da Isra'ila ta kai kan Gaza, kamar yadda ma'aikatar lafiyar Hamas ta shaida.

    Sa'oi bayan nan rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kakkaɓo wasu jiragen roka uku da Hamas ta ce ta harba a Tel Aviv.

    Lamarin ya zo ne bayan da Isra'ila ta koma yin luguden wuta a zirin cikin makon nan, inda hare-haren suka kashe fiye da mutum 430 cikin kwana biyu da suka gabata, a cewar ma'aikatar lafiyar.

    Rundunar sojin Isra'ila, IDF ta ce ta soma kai farmaki ta ƙasa a arewacin Gaza. An ɗan samu raguwar kai hare-hare tun watan Janairu lokacin da yarjejeniyar tsagaita wuta ta soma aiki.

    Isra'ila ta koma kai hare-hare a ranar Talata yayin da tattaunawar tsawaita yarjejeniyar ta fuskanci cikasa, inda ta yi gargaɗi cewa za su zafafa hare-hare har sai Hamas ta saki ragowra mutanen da take tsare da su.

    Isra'ila ta ce har yanzu Hamas tana riƙe da mutum 59, wasu 24 kuma ana tunanan suna nan da ransu.

    Kakakin IDF, Kanar Avichay Adraee ya ce Hamas ta harba rokoki uku daga kudancin Gaza. An kakkaɓo ɗaya daga cikinsu, sauran biyun kuma suka faɗa wani fili, kamar yadda ya wallafa a shafin X.

  13. Majalisar Dattawa ta amince da ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers

    Godswill Akpabio

    Asalin hoton, Office of the Senate President

    Majalsiar Dattawa ta amince da dokar ta-ɓaci da shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ayyana a kan jihar Rivers a ranar Talata.

    Majalisar dai ta shiga tattaunawar sirri bayan da shugaban majalisar Godswill Akpabio ya karantar wasiƙar a zauren.

    Shugaban masu rinjaye na majalisar, Sanata Opeyemi Bamidele ne ya karanta buƙatar shiga tattaunawar ta sirri bisa dogaro da doka mai 135 ta kundin majalisar.

    Shugaban marasa rinjaye, Sanata Abba Moro ne ya amince da shiga ganawar sirrin.

    Da ma dai majalisar wakilai ta amince da wannan dokar ta ta-ɓaci a ranar Alhamis.

  14. Ƴanbindiga sun yi garkuwa da gomman fasinjoji a Habasha

    Bindiga

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƴanbindiga sun yi garkuwa da gomman fasinjoji da suka taso daga Addis Ababa, a yankin Oromia da ke ƙasar Habasha.

    Lamarin ya auku ne a Ali Doro, kusa da inda aka sace ɗaliban jami'a kusan 100 a lokacin da suke hanyar komawa ɗakunan kwanansu a watan Yulin bara.

    Waɗanda suka tsira da hukumomin yankin sun ɗaura alhakin sace fasinjojin a kan ƙungiyar Oromo wato OLA, wadda ta ƴantawaye ce da suke da ƙarfi a yankin.

    Sai dai ƙungiyar ta fito ta musanta zargin, inda ta ce ba ta da hannu a lamarin.

    Ta ce ita ma ta samu labari, amma "za ta gudanar da bincike."

    Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton gwamnatin ƙasar ba ta ce komai ba.

    Garkuwa da mutane - ciki har da fasinjoji - ya fara zama ruwan dare a yankin, inda suke sace mutane domin karɓar kuɗin fansa.

  15. Babbar jam'iyyar hamayya a Turkiya ta soki kamen Imamoglu

    Babbar jamiyyar hammaya a ƙasar Turkiyya ta bayyana kamen da aka yi wa magajin garin Istanbul Ekrem Imamoğlu a matsayin juyin mulki.

    Ana dai kallon Mista Imamoğlu a matsayin babban abokin hammaya na shugaba Recep Tayyip Erdogan.

    Daya ke magana da BBC, mataimakin shugaban jam'iyyar Republicans ya ce tsare shi da aka yi babban koma baya ne ga mulkin dimokuraɗiyya.

    Mista Imamoğlu da wasu mutane na fuskantar tuhume-tuhume ciki har da rashawa.

  16. Majalisar Wakilan Najeriya ta amince da ayyana dokar ta-ɓaci a Rivers

    Kakakin majalisar wakilan Najeriya, Tajuddeen Abbas

    Asalin hoton, House of Reps/Facebook

    Bayanan hoto, Kakakin majalisar wakilan Najeriya, Tajuddeen Abbas

    Majalisar wakilan Najeriya ta goyi bayan ayyana dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Tinubu ya yi a jihar Rivers mai fama da rikicin siyasa.

    A ranar Talata ne Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Rivers tare da dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Ngozi Odu da ƴan majalisar dokokin jihar Rivers tsawon wata shida sakamakon rikicin da jihar ta faɗa.

    Kwana biyu bayan ɗaukan matakin ne Tinubu ya aike da takarda zuwa ga majalisar dokoki inda yake neman amincewarsu ga matakin da ya ɗauka.

    A zaman da majalisar wakilai ta yi a dazun nan, kakakin majalisar wakilan, Tajuddeen Abbas ya karanto wasiƙar da Tinubu ya aike masu.

    Ƴanmajalisar sun amince, da gagarumin rinjaye, matakin Tinubu na ayyana dokar ta-ɓacin.

    A cewar kakakin majalisar, ƴanmajalisa 240 ne suka halarci zaman, hakan na nufin an samu adadin ƴanmajalisar da ake buƙata wajen amincewa da duka wani ƙudiri.

    Matakin shugaba Tinubu dai ya yamutsa hazo a Najeriya inda al'ummar ƙasar ke tsokaci game da hurumi ko rashin hurumin shugaban ƙasar ya ɗauki irin wannan matsaya.

    Ko a baya-bayan nan, wasu manyan ƴanadawa a Najeriya sun soki matakin da suka kira saɓa kundin tsarin mulkin ƙasar tare kuma da kira ga majalisar dokokin ƙasar da ta yi watsi da ƙudirin.

  17. Manyan ƴan adawa a Najeriya sun yi fatali da dokar ta-ɓaci a Rivers

    Hoton manyan ƴan adawa a Najeriya

    Asalin hoton, Imran WakilI/X

    Bayanan hoto, Hoton manyan ƴan adawa a Najeriya

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El Rufai da ɗantakarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam'iyyar Labour, Peter Obi sun yi fatali da matakin Shugaban Najeria na ƙaƙaba dokar ta-ɓaci a jihar Rivers.

    El Rufai da sauran jagororin jam'iyyun hamayya sun buƙaci Majalisar dokokin Najeriya ta yi watsi da ƙudirin.

    A ranar Talata ne Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers inda ya dakatar da Gwamna Siiminalayi Fubara da mataimakiyarsa da mambobin majalisar dokokin jihar.

    Shi ma ɗantakarar shugaban ƙasa a 2023 ƙarkashin inuwar PDP, Atiku Abubakar, a jawabin a ya yi ranar Alhamis, ya zargi Tinubu da nuna ɓangaranci.

    Atiku Abubakar ya kuma nemi Shugaba Tinubu da ya janye matakin wanda ba ya bisa kundin tsarin mulkin ƙasa sannan ya maido da zaɓaɓɓn gwamna da mataimakiyarsa da sauran mutanen da aka dakatar kan kujerarsu.

    A cewarsa sun yi tur da matakin sannan sun yi kira ga ƴan Najeriya da su soki ƙudirin wanda ya saɓawa kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma dimokraɗiyya.

    • Mece ce dokar ta-ɓaci kuma me kundin tsarin mulkin Najeriya ya ce a kan ta?
    • Me ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers ke nufi?
  18. Hotunan haɗarin babbar mota da ya kashe mutum aƙalla 30 a Abuja

    Wata babbar motar kaya ta Kamfanin Dangote mai amfani da iskar gas da ke ɗauke da siminti ta afka kan motoci fiye da 14 kuma ta kashe mutum aƙalla 30 a jiya Laraba a Abuja.

    Kwamandan jami'an VIO a yankin Kugbo, Shehu Dalhatu ne ya shaida hakan.

    haɗarin babbar mota
    Bayanan hoto, Babbar motar Dangote maƙare da siminti
    haɗarin babbar mota
    Bayanan hoto, Jam'ian tsaro daban-daban a wurin da haɗarin ya afku
    haɗarin babbar mota
    Bayanan hoto, Sauran da ya rage daga wata mota da ta ƙone
    haɗarin babbar mota
    Bayanan hoto, Ma'aikata zaune a kan motar kashe gobara
    haɗarin babbar mota
    Bayanan hoto, Wasu motoci da suka ƙone a haɗarin
    haɗarin babbar mota
    Bayanan hoto, Wata mota da ta yi haɗari da wasu ƴan kallo
  19. Aƙalla mutum 6 sun mutu sakamakon haɗarin babbar mota a Abuja - Ƴansanda

    ...

    Rundunar ƴansandan babban birnin Najeriya Abuja ta tabbatar da mutuwar mutane shida da ƙonewar motoci 14 bayan wata babbar mota ta kama da wuta a yankin Karu.

    Kakakin rundunar ƴansandan SP Josephine Adeh wadda ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce ibtila'in ya faru ne a jiya laraba da ƙarfe 6:58 na yamma bayan wata babbar mota da ke maƙare da siminti ta ƙwace ta faɗa kan motocin da ke maƙale cikin cunkoso ababen hawa kusa da gadar Nyanya.

    Ta ce ma'aikatan ceto sun yi gaggawar isa wurin da ke cike da baƙin hayaƙi da tsananin zafi domin ceto waɗanda suka maƙale inda ta ce an samu nasarar zaƙulo mutane shida, sai dai bayan kai su asibiti likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.

    Kakakin rundunar ta kuma ce tare da haɗin gwiwar ƴansanda da ma'aikatan kashe gobara da ma wasu jam'ian tsaro an samu nasarar kashe gobarar.

    Rundunar ƴansandan Abuja ta kuma miƙa ta'aziyyarta ga iyalan waɗanda iftila'in ya shafa tare da tabbatarwa da alumma cewa za a gudanar da cikakken bincike kan sanadin iftila'in da kuma yadda za a kare sake afkuwar irinsa.

  20. Manyan ƙasashe za su gana kan kafa runduna ta musamman a Ukraine

    A yau Alhamis ne manyan hafsoshin soja daga ƙasashen da ke shirin kafa rundunar wanzar da zaman lafiya a Ukraine za su gana a Birtaniya.

    Ana tsamanin ƙasashe fiye da 20 ne za su shiga cikin abinda Firaministan Birtaniya Keir Starmer ya kira ''ƙawancen masu son su taimaka''.

    Ana dai sa rai taron wanda zai gudana ƙarƙashin jagorancin Birtaniya da Faransa zai maida hanakali ne kan yadda rundunar wanzar da zaman lafiya ta ƙasashen yamma za ta gudanar da ayyukanta.

    Shugaba Putin na Rasha dai ya ce ƙasarsa ba za ta amince da kasancewar dakarun kungiyar tsaro ta NATO a Ukarain ba.