Ba ma zumuɗin ƙulla alaƙar zaman lafiya da Iran - Pete Hegseth
Sakataren tsaron Amurka, Pete Heg-seth, ya ce Washington ba ta zumuɗi wajen kulla yarjejeniya zaman lafiya da Iran.
Yayin da yake magana a wani taron manema labarai, ya yi gargadin cewa toshe mashigar Hormuz na ƙara tsananta, kuma lamarin na shafar duniya baki ɗaya. Ya ce makomar kawo ƙarshen taƙaddamar na hannun Iran.
Wannan furuci na nuna yadda ake samun maganganu masu karo da juna daga Amurka, bayan da Shugaban ta Donald Trump ya ce ya tsawaita yarjejeniyar tsagaita wutar, ba tare da wani wa'adi ba a farkon makon nan.
Kafafen watsa labaran gwamnatin Iran sun ce ministan harkokin wajen ƙasar, Abbas Aragh-chi, na kan hanyarsa ta zuwa Pakistan, wadda ke shirin karɓar baƙuncin zagaye na biyu na tattaunawar zaman lafiya.