Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 28/11/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 28/11/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammad da Aisha Aliyu Jaafar da Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Ƙananan hukumomi 9 ne ke fama da matsalar tsaro - Gwamnan Kano

    Abba Kabir Yusuf

    Asalin hoton, Abba Kabir/Facebook

    Gwamnan jihar Kano da ke arewacin Najeriya Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatin sa ta mayar da hankali wajen tunkarar ƙaruwar matsalolin tsaro a jihar, kamar ayyukan ta'addanci da satar mutane da kuma satar shanu a wasu ƙananan hukumomi.

    Da ya ke magana a taron majalisar zartarwa karo na 34 a fadar gwamnatin jihar, gwamna Kabir ya ce gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro domin magance matsalar da ke tasowa da dawo da zaman lafiya.

    Ya ce ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Kunchi da Tsanyawa da Gwarzo da Kabo da Sumaila da Shanono da TudunWada da Doguwa da Rogo, inda ya bayar da tabbacin cewa ana ayyukan haɗin gwiwa domin toshe hanyoyin da ɓata garin ke amfani wajen shigowa.

    A farkon makon nan ne dai wasu ƴan bindiga suka sace mutum 18 a wasu ƙayuka uku da ke yankin ƙaramar hukumar Tsanyawa a jihar.

  2. An ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Guinea

    ...

    Asalin hoton, AFP

    An fara yaƙin neman zaɓe a hukumance a ƙasar Guinea gabanin zaɓen shugaban ƙasa da za a yi a ranar 28 ga watan Disamba.

    Ƴan takarar shugaban ƙasa 9 da suka haɗa da shugaban soji, Janar Mamady Doumbouya, za su kewaya sassan ƙasar da ke yankin yammacin Afirka don shawo kan masu son kaɗa ƙuri'a har zuwa ranar 25 ga watan Disamba.

    Ko da yake Janar Doumbouya yana takara ne a matsayin mai zaman kansa, amma yana da goyon bayan wata ƙungiya mai ɗauke da sunan sa: "The Generation for Modernity and Development (GMD)."

    Firaminista Bah Oury ne zai jagoranci yaƙin neman zaɓensa, kuma ministoci biyu za su taimaka masa.

    Shekaru huɗu da suka gabata, bayan hambarar da tsohon shugaban ƙasar Alpha Condé, Janar Doumbouya ya yi alƙawarin miƙa mulki ga farar hula, yana mai cewa, "Da ni da duk wani ɗan majalisar ministoci ba za mu nemi takarar komai ba... A matsayinmu na sojoji, muna daraja alƙawuran da mu ka ɗauka sosai."

    Yanzu dai ana gudanar da zaɓen ne a ƙarƙashin sabon kundin tsarin mulkin ƙasar wanda ya bai wa jagoran juyin mulkin damar tsayawa takarar shugabancin ƙasar.

    An buƙaci ƴan takarar shugaban ƙasa su biya dala dubu ɗari.

    Za a kuma gudanar da wannan zaɓen ne ba tare da wasu manyan mutane da ke zaune a wajen ƙasar a halin yanzu.

  3. Gwamnatin Kano na neman a kama Ganduje

    Ganduje

    Asalin hoton, PT

    Majalisar zartaswar jihar Kano ta yi kira da a gaggauta gudanar da bincike tare da kama tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bisa wasu kalamai da ta bayyana a matsayin tsokana da kuma tada zaune tsaye kan matsalar tsaro a jihar.

    Hakan ya biyo bayan tattaunawa ne a taron majalisar zartarwa karo na 34 da aka gudanar a ranar Alhamis a gidan gwamnatin jihar Kano, inda ƴan majalisar suka yi nazari kan kalaman Ganduje da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin na baya-bayan nan, inda suka yi zargin cewa Kano na kara fuskantar matsalar ƴan fashi da kuma bayyana shirin ɗaukar mutane 12,000 aikin ƴan sandan rundunar tsaro mai suna Khairul Nas.

    Da yake yiwa manema labarai ƙarin haske game da sakamakon taron a ranar Juma’a, kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce kalaman na iya kawo cikas ga ƙoƙarin tabbatar da tsaro da gwamnatin jihar da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi.

    Majalisar ta ƙara da cewa, ƙasa da sa'o'i 48 bayan an yi waɗannan kalamai, wasu da ake zargin ƴan bindiga ne suka kutsa kai cikin wasu al'ummomin kan iyaka a jihar - lamarin da ta ce "ya sanya ayar tambaya kan ko an furta kalaman tare da wata masaniya ce ko kuma suna da alaƙa da harin."

    “Ba mu san abin da Ganduje ke nufi da waɗannan kalamai ba saboda haka muna kira da a kama shi, dole ne a bincike shi saboda ba za mu iya kallon sa yana kawo mana cikas a zaman lafiya a jihar ba.” in ji shi

  4. An yi jana'izar Sheikh Dahiru Bauchi cikin juyayi

    Bauchi

    An yi jana'izar fitaccen malamin addinin Musuluncin Sheikh Dahiru Usman Bauchi ranar Juma'a, wanda ya rasu ranar Alhamis.

    An yi wa malamin sallah a masallacin Idi na garin Bauchi kafin a binne shi a masallacinsa da ke garin da misalin ƙarfe 6:45.

    Wakilin BBC ya ce dandazon mutanen da suka taru a kofar shiga masallacin ta sa sai da jami'an tsaro suka kafa shingaye kafin a iya shigar da shi wurin binnewar.

    Kazalika, wasu daga cikin iyalansa ba su samu shiga wurin ƙabarin ba saboda cikowar mutanen.

    Sheikh Shariff Ibrahim Saleh ne ya jagoranci yi waa malamin sallar jana'iza, kuma an binne shi ne kusa da wasu daga cikin iyalansa da suka rasu a baya.

    Sheikh Dahiru wanda jagora ne na darikar Tijjaniyya ya rasu yana da shekaru 98 a kalandar miladiyya, a kalandar Musulunci kuma yana da shekara 100 da ƴan watanni.

    Shehin malamin ya rasu ne a asibitin sojojin sama da ke jihar Bauchi bayan gajeriyar jinya.

    Ɗan marigayin, Naziru Dahiru Bauchi, ya faɗa wa BBC cewa an ajiye da gawar shehun a asibitin da ya rasu kafin lokacin da za a yi masa sallah a kuma kai shi makwancinsa.

  5. An shigar da gawar Shehi wurin da za a binne ta

    An shigar da gawar Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi masalacinsa da ke garin Bauchi, inda za a binne shi.

    Jana'izar Shehi
    Jana'izar Shehi
  6. Yadda aka yi sallar jana'izar Shehi

    ...

    Asalin hoton, Kano State Government

    ...

    Asalin hoton, Kano State Government

    ...

    Asalin hoton, Kano State Government

  7. Abu biyu da shehi yake jaddada mana lokacin karatu - Jikan Ɗahiru Bauchi

    Jikan Sheikh Dahiru Bauchi, Ibrahim Abubakar Tahir, ya ce yana alfaharin samun damar koyon karatu daga kakansa duk da cewa a lokacin da aka haife shi malamin ya manyanta.

    Ya kuma bayyana wasu shawarwari biyu na musamman da kakansa ke nanata musu idan yaransa za su tafi makaranta.

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon
  8. Yadda jama'a suka halarci jana'izar Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi

    Bauchi
    Bauchi
    Bauchi
    Bauchi
  9. Mahalarta jana'izar Dahiru Bauchi

    Jana'izar Dahiru Bauchi

    Dubun dubatar mabiya da masoya Sheikh Dahiru Usman Bauchi ne suka taru a birnin Bauchi a yammacin nan domin shaida yadda za a yi wa malamin sutura.

    Daga cikin 'yansiyasa da manyan jami'an gwamnati da suka halarci wurin akwai Mataimakin Shugaban Najeriya Kashim Shettima, da Gwamnan Kano Abba Kabir, da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar.

    Sauran sun ƙunshi Gwamnan Neja Umaru Bago, da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro Nuhu Ribadu, da tsohon Gwamnan Bauchi Ahmed Muazu, da Sanata Abdulaziz Yari.

  10. Jana'izar Sheikh Dahiru Bauchi kai-tsaye

    An fara gudanar da jana'izar Sheikh Dahiru Bauchi a garin Bauchi da ke arewa maso gabashin Najeriya.

    Kuna iya bin yadda jana'izar ke gudana a shafinmu na Facebook kai-tsaye a wannan adireshi da ke ƙasa.

  11. Dandazon jama'a a filin idi domin jana'izar Sheikh Ɗahiru Bauchi, Jana'izar Sheikh Ɗahiru Bauchi

    dandazon jama'a
    dandazon jama'a
  12. Yawan aikin Hajjin Sheikh Dahiru Bauchi

    shehi a yayin aiki Hajji

    Asalin hoton, Aminu Ɗahiru Bauchi

    A 2019, Sheikh Dahiru Bauchi ya shaida wa BBC cewa "tun daga shekarar 1970 kawo yau sau daya ne kawai ban je aikin Hajji ba."

    Hakan na nufin ya yi aikin hajji sau 48 ya zuwa 2019 ɗin kenan.

  13. Kashim Shettima ya isa Bauchi halartar jana'izar Sheikh Ɗahiru Bauchi, Jana'izar Ɗahiru Bauchi

    ..

    Asalin hoton, Stanley Kingsley Nkwocha/ Facebook

    Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya isa jihar Bauchi domin halartar janaizar fitaccen malamin addinin nan da ya rasu a jiya Alhamis, Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

    Mataimakin shugaban ƙasar ya sami tarba ne daga gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad da kuma na jihar Neja Umar Bago wanda tuni shi ma ya isa jihar.

    Ana sa ran nan gaba kaɗan ne za a yi jana'izar marigayin a wani filin idi da ke jihar Bauchi, kafin a kai shi makwancinsa da ke babban massalacinsa.

    ..

    Asalin hoton, Stanley Kingsley Nkwocha/ Facebook

  14. Harsuna biyar da Shehi ke ji

    ..

    Asalin hoton, AMINU DAHIRU BAUCHI

    A tattaunawar sa da BBC, Sheikh Dahiru Bauchi ya ce shi dai Bafulatani ne kuma ko an ji ya na Fulatanci babu mamaki.

    '' Mahaifina yana da tsangaya a ƙasar Borno inda yake da almajirai Hausawa da Barebari, saboda haka tun a lokacin na iya Hausa da Barbarci kuma tun ina karami na tashi da wadannan.''

    Ya kuma ce da ya girma ya iya Larabci kaɗan da yaren Wolof na su Shehi Nyass da Bolanci.

    Wani sanannen abu ne cewa Shehu Ɗahiru Usman Bauchi na gudanar da karatukansa ne a harshen Hausa.

  15. Lakurawa sun hallaka jami'an hukumar shige da fice 3 a Kebbi

    yan bindiga

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a jihar Kebbin Najeriya sun tabbatar da mutuwar jami'an hukumar shige-da-fice ta kasar su uku a cikin wani hari da mayakan Lakurawa suka kai kan gidajen kwanansu.

    An dai kai harin ne jiya da dare a kauyen Bakin ruwa na Karamar Hukumar Bagudo da ke da iyaka da jamhuriyar Benin.

    Kwamishinan tsaro da lamurran cikin gida na jihar Haliru Aliyu Wasagu, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce ƴan bindigar sun cinna wa gidajen ma'aikatan wuta ne cikin daren, sannan bayan sun fito daga gidan kuma suka harbe su har aka kashe 3 tare da jikkata ɗaya.

    Ya kuma ce an tura jam'ian tsaro yankin domin su maido da zaman lafiya, tare da farauto waɗanda suka aikata ta'asar.

    Aliyu Wasagu ya ce zuwa yanzu ba a san dalilin da ya sa suka kai wa jam'ian tsaron hari ba, sai dai ya ce dama mayaƙan Lakurawa kan kai wa jami'an tsaro hari, amma ana gudanar da bincike.

    Ko a watan Yuni ma sun kashe ƴan sanda uku a jihar, a kwanakin baya kuma sun hallaka wasu jami'an kwastam.

  16. Karatun da Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya yi

    Sheikh Dahiru Bauchi ya na addu'a

    Sheikh Dahiru ya ce ya haddace kur'ani a hannun mahaifinsa Alhaji Usman dan Alhaji Adam ne domin shi ma mahaddacin alkur'ani ne.

    Daga nan ne ya tura shi wurin malamai da dama domin tilawa, "kuma Alhamdulillahi na kan ji mutane na karin gishiri suna kira na gwani," in ji Malam.

    Malam ya je Bauchi domin karatu. Malaman da ya yi karatu a hannunsu sun hada da Malam Ahmadu na Sabon gari da Gwani dan Fika da malam Alhaji na Gombe da dai sauran su.

    Ya kara da cewa: "Ba gaskiya ba ne cewa na yi karatu wurin Shehi Nasiru Kabara. Malam Abubakar Gumi ne ya yi karatu wurin Shehi Nasiru Kabara.

    "Na kuma karbi darikar Tijjaniya a hannun mahaifina."

    "Bayan na haddace Alkur'ani inda ake kira na gwani ko gangaran, na rubuta Alkur'ani na farko na bai wa babana kuma malamina kyauta''. in ji shi.

    "Na kuma rubuta na biyu wasu sun manta. Na fara rubuta na uku amma ban gama ba har yanzu.

    "Ina da matsalar agana a idanuna dalilin da ya sa ba ni da nishadi kan duk abin da za a kalla," a cewarsa.

    Malamin ya ce matsalar idanun ce ta sa bai yi wasu rubuce-rubuce ba a fannoni da dama.

  17. MDD ta nemi a gudanar da bincike kan kisan Falasɗinawa bayan sun miƙa wuya

    Hukumar kare haƙƙin bil'adama ta Majalisar ɗinkin duniya ta yi kiran a gudanar da bincike kan kisan wasu Falasɗinawa biyu da jami'an tsaron Isra'ila suka yi bayan mutanen sun miƙa wuya.

    Hukumar ta ce ta matuƙar girgiza kan abin da ta kira kisa ba gaira ba dalili da aka yi a Jenin da ke yankin gaɓar Yamma da Kogin Jordan.

    A cikin wani bidiyo an ga maza Falasdinawa biyu na fitowa daga wani gini hannuwansu a sama yayin da 'yansandan iyaka na Isra'ila suka kewaye su.

    Daga nan sai jami'an suka harbe su dab-da-dab.

    Rundunar soji da 'yansandan Isra'ila sun ce mutanen 'yan ta'adda ne da ake nemansu, kuma ana gudanar da bincike kan lamarin.

  18. Dangantakar Shehi da Sheikh Ibrahim Inyass

    Sheikh Dahiru Bauchi

    Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya shaida wa BBC cewa, baya ga kasancewa almajirin Sheikh Ibrahim Inyass, akwai karin dangantaka mai ƙarfi a tsakaninsu.

    Ya ce: ''Alhamdulillah baya ga zama almajirin Sheik Ibrahim na kuma zama khadiminsa, kana na zama surukinsa, don na auri 'ya'yansa har sau biyu, na auri ɗaya bayan ta rasu ya sake bani auren ɗaya.''

    Kana malamin ya ce baya ga haka, yana ƙauna tare da mutunta malamai a ko ina suke, musamman malaman Tijjaniyya.

    ''Babu abin da ke faranta min rai irin na ga Musulunci ya bunƙasa, in ga darikar Tijjaniyya ta bunƙasa,'' in ji malamin.

  19. Gwamnatin Bauchi ta ayyana hutu yau Juma'a

    gwamnan Bauchi

    Gwamnatin Jihar Bauchi da ke Arewacin Najeriya ta ayyana hutu a yau Juma'a domin alhinin rasuwar marigayi Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a jiya Alhamis.

    A cikin wata sanarwa da mai bai wa gwamnan shawara kan yaɗa labarai Mukhtar Gidado ya fitar, an sanar da hutun ne domin bayar da dama ga ma'aikata da ɗalibai da ma ƴan jihar bakiɗaya su samu damar halartar jana'izar marigayin.

    A yau juma'a ne za a yi wa Sheikh Ɗahiru Bauchi Sallar Jaza'iza a filin idi da ke jihar, sannan a binne shi a massalincin juma'arsa.

    Tuni dai alumma ke ta tururuwar isa jihar daga sauran jihohi ƙasar da ƙasashen waje, yayin da su ma alummar jihar ke tururuwar isa wurin da za a yi sallar.

  20. Wakilin BBC ya tattaro bayanan halin da ake ciki a Bauchi, Jana'izar Sheikh Ɗahiru Bauchi

    Bayanan bidiyo, BBC ta tattaro kan halin da ake ciki a birnin Bauchi wajen jana'izar Sheikh Dahiru Bauchi

    Wakilin BBC ya ce za a yi wa Sheikh Ɗahiru Bauchi ne a masallacin Idi da ke Bauchi, sannan kuma daga bisani a binne shi a masallacin Juma'ar da Shehin ya gina da ke kusa da gidansa.