Najeriya ta yi nasara a wasan farko

Asalin hoton, Getty Images
Mun gode ƙwarai da kuka kasance tare da mu yayin da Najeriya da Tanzaniya suka buga wasansu na farko a gasar cin kofin Afirka ta 2025 a ƙasar Moroko, inda Najeriya ta yi nasara.
Najeriya za ta yi wasanta na biyu da ƙasar Tunisiya a birnin Fes ranar Asabar da yamma.
Ita kuma Tanzaniya za ta yi karawa ta biyu da Uganda a birnin Rabat a ranar ta Asabar da yamma.
Za ku iya karanta bayanai kan gasar cin kofin Afirka a shafinmu na bbchausa.com da kuma shafukanmu na sada zumunta.
Ku shiga zaurenmu na WhatsApp domin samun bayanai da ɗumi-ɗumi kan AFCON da ma sauran abubuwan da ke faruwa a doron duniya.








