Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. 'An kama shugaban ƙungiyar safarar miyagun ƙwayoyi a Equador'

    Shugaban Equador, Daniel Noboa, ya ce an kama shugaban ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi mafi girma a ƙasar, a wani samame na haɗin gwiwa da ƴan sandan Sifaniya.

    Mista Noboa ya sanar da kama Wilmer "Pipo" Chavarria ne a wani sako da ya wallafa a shafukan sada zumuta inda ya ce shugaban ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyin ya ɓoye a Turai, inda yake ci gaba da gudanar da harkokin ƙungiyar tasu, bayan aka yi ƙaryar cewa ya mutu.

    Ƴan Equador na kaɗa ƙuri'ar raba gardama kan abubuwan da suka shafi tsaro - da suka haɗa da a bar sojojin ƙasashen waje su kafa sansani ƙasar.

    Ƙasar da ke Kudancin Amurka ta sha fama da rikice-rikice a ƴan shekarun nan, lamarin da ake alaƙantawa da ayyukan masu safarar hodar ibilis.

  2. 'Za mu tsara kasafin kuɗin 2026 kan buƙatun al'ummar Sokoto'

    Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu ya ce gwamnatinsa za ta tsara kasafin kuɗin jihar na 2026 bisa buƙatun da al'ummar jihar suka gabatar.

    Yayin da yake jawabi a wani taron tattaunawa kan kasafin kuɗin jihar na 2026, gwamnan jihar Ahmad Aliyu ya ce ingantaccenkasafin kuɗi shi ne wanda ya fito daga buƙatun jama’a, ba kawai daga teburin gwamnati ba.

    “Mun zo nan ne domin sauraron ku, domin ku ne tushen abin da za mu tsara,” in ji Gwamnan.

    Taron, ya ƙunshi manyan jami’an gwam­nati da shugabannin ƙananan hukumomi, masu ruwa da tsaki, ƙungiyoyin matasa, da na mata.

    Gwamnatin jihar ta ce ta shirya taron ne da nufin shigar da ra’ayoyin al'umma cikin kasafin kuɗin 2026.

    Gwamna Ahmad Aliyu ya ce kasafin na 2026 - da zai gabatar nan ba da jimawa ba - zai fi mayar da hankali kan ayyuka masu tasiri ga rayuwar al’umma.

    Ahmad Aliyu ya ce kasafin kuɗin shekarar mai zuwa zai mayar da hankali ne kan manyan abubuwa guda huɗu da suka haɗa da bunƙasa tattalin arziki da gina abubuwan more rayuwa da kuma samar da tsaro da zaman lafiya.

  3. Mutum 32 sun mutu bayan ruftawar mahaƙar ma'adinai a DR Kongo

    Jami'ai a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo sun ce aƙalla masu hakar ma'adinai 32 ne suka mutu bayan da wata gada ta ruguje a wata mahaƙar ma'adinan cobalt a kudu maso gabashin ƙasar.

    Rahotanni sun ce an hana shiga wurin ne saboda ruwan sama mai yawa da kuma haɗarin zaftarewar ƙasa.

    Masu haƙar ma'adinan sun kasance a wurin ba tare da izini ba a lokacin da lamarin ya faru.

    Rahotanni daga yankin sun ce ana ci gaba da gudanar da ayyukan ceto.

  4. Nakan yi kuka a duk lokacin da na ji labarin kisa - Akpabio

    Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Godswill Akpabio ya ce alhakin gwmanati ne maido da zaman lafiya da haɗin kai a jihar Filato.

    Yayin da yake jawabi a taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar APC a jihar ranar Asabar a birnin Jos, Akpabio ya ce babu wani daga waje da zai kawo wa ƙasar zaman lafiya da kwanciyar hankali.

    Jaridar Daily Trust ta ambato shugaban majalisar dattawan na kira ga ƴan Najeriya su rungumi tsarin zaman lafiya.

    Ya kuma jaddada abin da ya kira ƙudurin shugaban ƙasar na magance matsalolin rikice-rikice a faɗin ƙasar.

    “Ina tsaye a nan domin wakiltar shugaban ƙasa, tare da tabbatar muke cewa zai yi duk mai yiwuwa domin samar da zaman lafiya, ba wasu mutane daga wajen ƙasarmu ne za su zo domin kawo mana zaman lafiya ba, mu ne za mu samar wa kanmu'', in ji shi.

    "Ina mai tabbatar wa da ƴan Filato cewa za mu warware muku matsalolinku. Nakan yi kuka a duk lokacin da na ji labarin cewa an kashe mutum, babba ko ƙarami".

  5. An kama wanda ake zargi da kai harin Delhi

    Hukumomin tsaro a Indiya sun ce sun kama wani mutum da aka zargi da hannu a harin da ya kashe mutane takwas da raunata wasu 20 a Delhi a makon jiya.

    Hukumar binciken sirri ta ƙasar ta ce sunan mutumin da aka kama ne a rigistar motar da aka kai harin da ita, don haka ana zarginsa da haɗa baki domin kai harin ƙunar baƙin wake.

    Wanda ake zargin mazaunin Kashmir ne, amma an kama shi ne a birnin Delhi.

    Gwamnatin Indiya ta ce harin na ta'adanci ne.

    Wannan ne karon farko da aka samu irin wannan harin a birnin Delhi, tun bayan wanda aka samu a 2011.

  6. Masu zanga-zanga sun yi wa taron sauyin yanayi tsinke a Brazil

    Dubban masu zanga-zanga sun yi wa wurin taron Majalisar Ɗinkin Duniya kan yanayi tsinke, wanda ke gudana a Brazil.

    Sun yi ta waƙe-waƙen "free the Amazon" (a kare amazon) yayin da suka isa wurin taron na COP30 a birnin Belem ɗauke da kwalaye iri-iri.

    Kazalika suna ɗauke da manyan gawawwaki na bogi waɗanda aka rubuta man fetur, da gawayi, da gas a jiki.

    Mazauna yankunan na asali kuma sun yi ɗaga kwalayen da ke cewa "mu ne amsar".

    Wannan ne karon farko tun 2021 da aka ƙyale masu zanga-zangar suke yin maci a wurin da ake yin taron na shekara-shekara.

  7. Jiragen 'yan cirani biyu sun kife a tekun Libya

    Wasu jiragen ruwa biyu ɗauke da mutanen da ke ƙoƙarin kaiwa ga nahiyar Turai sun kife a gaɓar ruwan Libya.

    Kungiyar agaji ta Red Crescent a kasar ta ce jirgi na farko na ɗauke da 'yan cirani 26 daga Bangladesh kuma ya kife ne a gabar ruwan Khoms da ke gabashin Tripoli. Akalla mutum huɗu aka tabbatar sun rasa mutu.

    Jirgi na biyu kuma na dauke da mutum 69 yawancinsu 'yan kasar Sudan, kuma har kawo yanzu ba a san adadin mutanen da suka mutu ba a jirgin.

    Jirgi na baya-bayan nan da ya kife shi ne na ranar Juma'a kuma ya kife ne kwana ɗaya bayan 'yan cirani fiye da 40 sun nitse a wani jirgi na daban a Libyan.

  8. 'Yan gudun hijira a Birtaniya za su shekara 20 kafin samun damar zama na dindindin

    Gwamnatin Birtaniya ta ce tana duba yiwuwar sauya manufofinta kan yadda ake neman mafaka a kasar a wani yunkuri na shawo kan karuwar damuwar da ake nunawa kan batun 'yancirani.

    A karkashin tsarin da take son bullo da shi, duk 'yan gudun hijirar da aka bai wa mafaka dole su jira har tsawon shekara 20 kafin su nemi damar zama ta dindindin a kasar.

    Sannan a tsawon shekarun kuma za a iya neman su koma ƙasasashensu na asali idan aka ga al'amura sun inganta a can.

    Bangaren masu sassaucin ra'ayi a kasar dai sun ce matakin bai yi tsauri sosai ba.

  9. DSS sun ce sun kama dillalin makamai a jihar Filato

    Rundunar 'yansandan farin kaya ta DSS a Najeriya ta ce ta yi nasarar kama wani dillalin makamai da ke yi wa 'yanbindiga safara zuwa jihar Filato mai fama da rikicin ƙabilanci.

    Cikin wata sanarwa a yau Lahadi, rundunar ta ce ta kama wanda take zargin a ranar Laraba bayan tattara bayanan sirri, kamar yadda shafin intanet na Channels TV ya ruwaito.

    Ta ce bayanai sun nuna cewa mutumin yana haɗawa da kuma safarar makaman a unguwar Mista Ali da ke ƙaramar hukumar Bassa a jihar ta Filato da ke arewa ta tsakiyar Najeriya.

    "Samamen ya ba mu damar kama mutumin mai suna Musa Abubakar, kuma ya amsa laifin haɗawa da safarar manyan makamai da harsasai ga ƙungiyoyin 'yanbindiga a Filato da wasu jihohin arewaci," a cewar sanarwar.

    A ƙarshen makon nan rundunar ta sanar da sake kama Abdulazeez Obadaki, wanda aka fi sani da Bomboy, bayan ya tsere daga Gidan Yarin Kuje a Abuja wanda ake zargi da hannu a hari kan cocin Owo da ke jihar Ondo.

  10. Yau Najeriya za ta kara da DR Congo

    Najeriya za ta kara da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo a wasan neman gurbin gasar Kofin Duniya ta 2026.

    Super Eagles ta kai karawar ta karshe tsakanin kasashen Afirka ne bayan doke Gabon 4-1 a ranar Alhamis, 13 ga watan Nuwamba.

    Wankin hula ya so ya kai Najeriya dare a wasan nata da Gabon, inda har aka kai ga yin karin lokaci, kafin daga baya Najeriya ta zura kwallaye uku da suka ba ta nasara.

    Ita kuwa DR Congo, kwallon da dan wasanta Chancel Mbemba ya ci ana dab da tashi ce ta ba ta damar zuwa wannan mataki.

    Za a kara tsakanin Najeriya da DR Congo ne a filin wasa na Stade Prince Moulay Abdellah a birnin Rabat na kasar Moroko da karfe 8:00 na dare agogon Najeriya.

    Wannan ne karon farko da Najeriya za ta kara da DR Congo tun bayan wasan sada zumunta da suka tashi 1-1 a shekarar 2018.

    Idan Najeriya ta yi rashin nasara ba za ta samu gurbin zuwa gasar Kofin Duniya ba, amma idan ta doke Congo za ta kai wasan ƙarshe na karawa tsakanin ƙasashen nahiyoyi daban-daban, kuma dole ne ta sake yin nasara a nan kafin samun gurbin gasar.

    A jerin karawar da aka yi a baya, DR Congo ta yi nasara kan Najeriya sau uku, Najeriya ta yi nasara sau biyu, da kuma canjaras ɗaya.

  11. Kabiru Tanimu Turaki: Wane ne sabon shugaban PDP na ƙasa?

    Kabiru Tanimu Turaki (SAN) ya zama shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa a ranar Asabar bayan lashe zaɓen da aka gudanar a babban taro na ƙasa a birnin Ibadan na jihar Oyo.

    Ya samu kuri'a 1,516 cikin 1, 834 da aka kaɗa, inda ya yi nasara kan Sanata Lado Danmarke wanda ya zo na biyu.

    • An haifi Kabiru Tanimu Turaki a ranar 3 ga watan Afrilun 1957 a Birnin Kebbi na jihar Kebbi
    • Ya karanta fannin shari'a a Jami'ar Jos kuma ya kammala a 1985. An kira shi zuwa majalisar lauyoyi ta Bar (Nigerian Bar) a 1986.
    • Ya zama Babban Lauyan Najeriya (Senior Advocate of Nigeria - SAN) a shekarar 2002, kuma shi ne shugaban kamfaninsa mai suna K.T Turaki & Co
    • Ya yi aiki a matsayin ministan ayyuka na musamman a ƙarƙashin tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan daga 2013 zuwa 2015. Ya kuma rike muƙamin ministan ƙwadago na riƙo, sannan ya shugabanci kwamitin shugaban Kasa kan tattaunawa da samar da zaman lafiya a Arewa
    • Kafin ya zama shugaban PDP, ya nemi takarar shugaban ƙasa a 2018 amma bai yi nasarar samun tikitin ba, sannan ya kasance shugaban ƙungiyar tsoffin ministocin PDP (PDP Former Ministers' Forum).
    • Yana riƙe da sarautun gargajiya da suka haɗa da Dan Masanin Gwandu da Zarumman Kabbi
  12. Babu sauran sakaci a jam'iyyarmu ta PDP - Kabiru Turaki

    Sabon shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa Kabiru Turaki ya nemi goyon bayan 'ya'yan jam'iyyar, yana mai cewa "babu sauran sakaci" a jam'iyyar.

    Turaki ya bayyana hakan ne a jawabin nasarar da ya yi bayan lashe zaɓen da aka yi yayin babban taron PDP na ƙasa a jihar Oyo ranar Asabar, wanda ya lashe da ƙuri'a 1,516 cikin 1, 834 da aka kaɗa.

    "Ina tabbatar muku amanar da kuka ba mu ba za mu ɗauke ta da wasa ba, babu wani sauran sakaci da kuma ƙwace wa 'yan Najeriya zaɓinsu," in ji shi.

    Ya ƙara da cewa nan gaba kaɗan zai duƙufa wajen ziyartar dukkan 'yan jam'iyyar da suke jin ba a yi musu daidai ba tare da tabbatar da adalci ga kowa.

  13. Zan bar PDP zuwa APC ranar Laraba - Gwamnan Taraba Kefas

    Gwamnan jihar Taraba a tsakiyar Najeriya ya sanar da cewa zai fice daga jam'iyyar PDP mai adawa zuwa All Progressives Congress (APC) ranar Laraba mai zuwa.

    Da yake magana yayin wata ziyara a filin wasa na Jolly Nyame ranar Asabar - inda nan ne wurin taron komawa APC din - Gwamna Agbu Kefas ya ce matakin komawa APC ɗin yana da alaƙa ne da ciyar da rayuwar mazauna Taraba, ba wai raɗin kansa ba.

    "Zan fita daga PDP zuwa APC ranar 19 ga watan Nuwamba a hukumance," in ji shi. "Wannan yunƙuri magana ce ta makomar al'ummar Taraba kuma muna mutane da yawa za su halarci bikin."

    Da ma gwamnan na cikin waɗanda ba su halaraci babban taron PDP na ƙasa da aka gudanar a birnin Ibadan ba ranar Asabar, inda ta zaɓi sababbin shugabanni. Sauran su ne Gwamnan Rivers Fubara da Adeleke na jihar Osun.

    Idan gwamnan ya fita daga jam'iyyar zai zama jihohin da PDP ke mulki sun koma takwas kenan, yayin da a baya-bayan nan gwamnonin Bayelsa da Delta suka koma APC ta Shugaba Tinubu mai mulki.

  14. Dubban matasa na zanga-zanga a Mexico kan matsalar tsaro

    Ana gudanar da zanga-zanga a birnin Mexico, inda dubban mutane ke nuna ɓacin rai kan karuwar tashe-tashen hankali da rashin tsaro da kuma adawa da gwamnatin Shugaba Claudia Sheinbaum.

    Hotunan da aka nuna na wajen sun nuna yadda masu zanga-zangar suka hamɓare shingayen karafan da aka sanya a harabar fadar shugabar kasar tare da jibge jami'an tsaro da dama.

    Matasa masu kiran kansu Gen Z ne suka shiryata, inda suke neman goyon bayan wasu kungiyoyi masu zaman kansu a kasar musamman wadanda suka fusata da kisan da aka yi wa Magajin Gari Uruapan Carlos Manzo.

    An kashe shi ne a yayin wani taro da ya halarta a farkon watan nan.

  15. Gwamnan Filato Muftwang ya ce ba shi goyon bayan korar Wike daga PDP

    Gwamnan jihar Filato a arewacin Najeriya, Caleb Muftwang, ya nisanta kansa daga matakin da jam'iyyarsu ta PDP mai adawa ta ɗauka na korar Ministan Abuja Nyesom Wike daga jam'iyyar.

    A jiya Asabar ne jam'iyyar ta kori ministan, wanda ya daɗe yana rigima da shugabancin jam'iyyar, da sakatarenta na ƙasa Samuel Anyanwu, da tsohon gwamnan Ekiti Ayo Fayose yayin babban taronta na ƙasa tana mai zargin su da yi mata zagon ƙasa.

    Cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa ya fitar, Muftwang ya ce majalisar gwamnonin PDP da kwamatin zartarwa ba su tattauna batun ba kafin a bijiro da shi yayin taron.

    Ya ƙara da cewa "korar jiga-jigan jam'iyyar a wannan lokaci mai muhimmanci ba tunani ne mai kyau ba wajen shawo kan rikicin da ya dabaibaye PDP".

    Kalaman Muftwang na zuwa ne jim kaɗan bayan Gwamnan Adamawa Ahmadu Fintiri shi ma ya ce bai goyi bayan dakatar da ministan da abokan siyasarsa ba.

  16. 'Yantawayen M23 da gwamnatin Kongo sun ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya

    Wakilan gwamnatin Jamhuriyar Dimokradiyyar Kongo da na 'yantawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a gabashin Kongo.

    An sanya hannun ne a Doha babban birnin Qatar bayan shiga tsakani da jami’an Qatar ɗin da Amurka da ƙungiyar Tarayyar Afirka suka yi.

    Yarjejeniyar ta ƙunshi tsagaita wuta da sakin fursunoni da kuma warware ainihin abin da ya janyo fadan, kamar rikici a kan albarkatun kasa da kuma zaman ɗarɗar da ake yi a lardin Kivu da ke gabashin Kongo.

    Wakilin BBC ya ce Kinshasa ta bukaci cewa dukkan sojojin Rwanda su bar yankunan Kongo da iyakoki, yayin da Kigali kuma ta ce hakan zai yiwu ne idan Kongo ta tarwatsa masu tayar da kayar bayanta.

    Fadan da 'yantawayen na M23 ke yi a Kongon ya tursasa wa miliyoyin mutane barin muhallansu da kuma haddasa kashe-kashe da dama.

  17. Barka

    Barkanmu da sake haɗuwa a shafin labarai kai-tsaye na ranar Lahadi.

    Za mu kawo rahotonni na abubuwan da ke faruwa a sassan dunya.