Hukumar ƙwallon Saudiyya ta gargaɗi Ronaldo

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar kula da gasar ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa ta Saudiyya, wato Saudi Pro League ta gargaɗi Cristiano Ronaldo kan cewa “babu wanda ya fi ƙarfin ƙungiyarsa – duk muhimmancinsa, balle ya ce shi zai yanke wa ƙungiyar hukunci”.
Hakan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tababa kan makomar fitaccen ɗan wasan a ƙungiyar Al-Nasr.
Ɗan wasan ɗan asalin ƙasar Portugal bai buga wasan da Al-Nassr ta yi ba a gasar ta Saudi Pro League da ƙungiyar Al-Riyad a ranar Litinin.
Jaridar A Bola ta Portugal ta ruwaito cewa Ronaldo ya ƙi buga wasan ne sanadiyyar rashin gamsuwa da yadda hukumar zuba jari ta Saudiyya ke tafiyar da lamurran ƙungiyar.
An shaida wa BBC cewa komawar ɗan wasa Karim Benzema zuwa ƙungiyar Al-Hilal daga Al-Ittihad a farkon makon nan na daga cikin abubuwan da suka tunzura Ronaldo a ƙungiyar Al-Nassr.
Benzema ya zura ƙwallo uku a wasa na farko da ya buga wa Al-Hilal ranar Alhamis lokacin da suka kara da ƙungiyar Al-Okhdood.
Ƙungiyar Al-Nassr da Al-Hilal duk suna ƙarƙashin kulawar hukuma ɗaya ce, kuma su ne ƙungiyoyin da suka fi samun nasara a gasar, inda suka lashe kofuna 19.

















