Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 26/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 26 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Dusar ƙanƙara ta mamaye Amurka ta katse wutar lantarki

    Ana ci gaba da fuskantar tsananin sanyi da zubar dusar kankanra a sassan Amurka inda aka samu daukewar wutar lantarki a wurare da dama da kuma soke tashi da saukar jirage dubu 11.

    Kusan gidaje da wuraren kasuwanci miliyan guda basu da wutar lantarki.

    Yanayin tsananin sanyi ya faro ne daga New Mexico zuwa Maine inda aƙalla a yanzu jihohin kasar 23 sun ayyana dokar ta baci.

    Jihohin da ke kudu maso gabashin ƙasar na shirin fuskantar mummunan yanayi na sanyi inda aka yi hasashen zubar dusar kankara mai yawan gaske a wasu yankuna na jihohin.

    Masu hasashen yanayi sun ce za a shafe kwanaki ana fuskantar tsananin sanyin sannan kuma zai haddasa asara da dama.

  2. Ganduje ya koma Abuja daga Landan 'don bikin karɓar' Abba zuwa APC

    Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, ya koma Najeriya daga Birtaniya a yau Litinin, yayin da jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ke shirin karɓar gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, bayan ficewarsa daga NNPP a makon da ya gabata.

    A yau ne ake sa ran gwamna Abba Kabir zai sanar da komawa jam'iyyar APC a hukumance bayan raba gari da ubangidansa a siyasa, Rabi'u Musa Kwankwaso, wanda shi ne jagoran jam’iyyar NNPP lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ke a tsakanin ɓangarorin siyasa a Kano, jiha mafi yawan al'umma a arewacin Najeriya.

    Wata sanarwa da Kwamared Muhammad Garba, shugaban ma’aikatan Abdullahi Ganduje, ya fitar, ta ce ana sa ran tsohon gwamnan "zai taka muhimmiyar rawa a bikin karɓar Gwamna Abba Kabir, wanda ake sa ran zai sauya sheƙa zuwa APC" a yau Litinin.

    Ganduje ya tafi Birtaniya ne domin halaratar bikin kammala karatun digiri na biyu na ‘yarsa Fatima Ganduje a jami’ar King’s College, London. wadda ta kammala karatunta a ranar Alhamis da ta gabata.

    A jiya Lahadi ne Sanusi Bature, mai magana da yawun gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya sanar da cewa gwamnan zai sake komawa jam'iyyar APC a yau Litinin.

    A ranar Juma'a ne Abba Kabir ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar NNPP da aka zaɓe shi a karkashinta a shekarar 2023.

    Gwamnan ya bayyana rikicin cikin gida da fifita ci gaban al'ummar jihar Kano a matsayin dalilansa na ficewa daga NNPP.

  3. Tinubu zai tafi Turkiyya a yau Litinin

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu zai yi tafiya a yau Litinin, 26 ga Janairu, zuwa ƙasar Turkiyya domin ziyarar aiki ta ƙasa, a wani yunkuri na ƙarfafa alaƙar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu.

    A cewar wata sanarwa da mai bai wa Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a jiya Lahadi, ziyarar na da nufin faɗaɗa haɗin gwiwa a muhimman fannoni da suka haɗa da tsaro da ilimi da ci gaban al’umma da kirkire-kirkire da kuma harkar sufurin jiragen sama.

    Sanarwar ta ce wannan ziyara na zuwa ne bayan ziyarar aiki da shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdoğan ya kai Najeriya a ranakun 19 zuwa 20 ga Oktoba, 2021, wadda ta ƙara ƙarfafa alaƙar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu.

    A yayin ziyarar, ana sa ran ƙasashen biyu za su gudanar da tattaunawar siyasa da diflomasiyya kan muhimman batutuwa da suka haɗa da harkokin kuɗi, sadarwa, kasuwanci da zuba jari.

    Daga cikin tawagar Shugaban Ƙasar da ke halartar tattaunawar diflomasiyyar akwai ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar da ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, SAN da ministan tsaro, Janar Christopher Musa, da Shugaban Kwamitin Tsaro na Majalisar Wakilai, Jimi Benson.

  4. Ofishin hukumar ƴan gudun hijirar Falasɗinawa a gaɓar yamma ya kama da wuta

    Hukumar kula da 'yan gudun hijirar Falasdinawa ta ce ginin shalkwatarta da ke Gabar yamma da kogin Jordan da aka fara rushewa yanzu yakama da wuta.

    A makon daya gabata ne mahukuntan Isra'ila suka lalata wanu ɓangare na ginin hukumar.

    Cikin wata sanarwa da ya sanya a shafinsa na X, shugaban hukumar Philippe Lazzarini,ya ce wutar da aka sanyawa ginin na su a yanzu shi ne hari na baya bayan nan da aka kai musu a wani yunƙuri na tarwatsa hukumar.

    Ba dai a bayar da cikakken bayani akan yadda wutar ta tashi a ofoshin hukumar ba.

  5. Lokuta bakwai da aka ɓaɓe tsakanin 'ubangida da yaronsa' a siyasar Najeriya

    Nan gaba a yau ne gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sanar da komawa jam'iyyar APC a hukumance bayan raba gari da ubangidansa a siyawa, Rabi'u Musa Kwankwaso, wanda shi ne jagoran jam’iyyar NNPP.

    A ranar Juma'a ne Abba Kabir ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar NNPP da aka zaɓe shi a karkashinta a shekarar 2023.

    Gwamnan ya bayyana rikicin cikin gida da fifita ci gaban al'ummar jihar Kano a matsayin dalilansa na ficewa daga NNPP.

    Tuni dai jam'iyyar ta yi masa martani, cikin wata sanarwa da ta fitar, inda ta bayyana matakin a matsayin rashin mutunta masu kaɗa ƙuri'ar da suka ba shi gagarumin goyon baya a zaɓen gwamna na 2023.

    Ba wannan ne karon farko da aka samu sabani, wanda ya kai ga ɓaɓewa tsakanin ubangida da yaronsa a siyasar Najeriya ba.

    Saɓani tsakanin ubangida da yaro a siyasar Najeriya abu ne da ya daɗe yana faruwa, inda akasari hakan ke faruwa bayan yaron ya hau mulki kuma ya fara ƙoƙarin cin gashin kansa.

  6. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Litinin

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.