Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 16/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 16/01/2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi, Aisha Babangida da Abdullahi Diginza

  1. Kotu za ta yanke hukunci kan tsohon shugaban ƙasar Koriya ta Kudu

    A yau ne wata kotu a Koriya ta Kudu zata yanke hukunci kan shari’ar da ake yi wa tsohon shugaban kasa, Yoon Suk Yeol, kan dokar sojin da ya sanya wadda ba ta yi tasiri ba.

    Idan aka same shi da laifin wasa da mulki, zai iya fuskantar hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 10.

    Haka zalika, tsohon shugaban zai fuskanci shari’o’i da dama, ciki har da tuhume-tuhume kan tarihi da ayyukan da ya yi yayin mulkinsa, wanda ya sa masu shigar da ƙara suka nemi a yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

    Kotun za ta tantance hujjojin da aka gabatar da kuma yadda dokokin kasa da kasa ke kallon irin wannan laifi, kafin ta yanke hukunci.

  2. Ba mu kawo sabon harajin cirewa da tura kuɗi ba - Hukumar harajin Najeriya

    Hukumar Haraji ta Najeriya NRS ta bayyana cewa rahotanni da ke yawo a wasu sassa na kafofin yaɗa labarai game da cewa an kawo sabon harajin cirewa da tura kuɗi wato VAT ba gaskiya bane.

    Hukumar ta ce wannan bayani na yaudara ne kuma babu sabuwar haraji i da aka kafa a kan kwastomomi aka ce wajibi ne sai sun biya.

    Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X.

    NRS ta bayyana cewa tun farko dama wannan haraji na aiki a ƙarkashin dokar haraji na Najeriya da aka kafa tun shekaru da dama inda bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi ke cire kuɗin gudanarwa, da na hidima da suka yi da sauran kuɗaden da suke cirewa, ba sabon haraji bane.

    Ta bayyana cewa duk wani bayanin da ke cewa gwamnati ta umarci bankuna da su fara cire harajin kashi 7.5 a kan kudin da aka cire ko aka tura da suka kai naira 100,000 ba dai dai bane.

    Saboda haka ne hukumar ta buƙaci jama’a da masu ruwa da tsaki da su daina yarda da labaran da ba su da tushe, su kuma dogara ga sanarwar hukumar kai tsaye don samun sahihin bayani.

  3. Martanin Atiku kan komawar ɗansa APC

    Ɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar ya ce shawarar da ɗansa Abba Atiku Abubakar ya yanke na barin jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC mai mulki mataki ne na ƙashin kansa.

    A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, Atiku ya ce a tsarin dimokuraɗiyya irin waɗannan lamuran ba sabon abu ba ne, ko da kuwa siyasa ta haɗu da alaƙar iyali.

    Atiku ya ƙara da cewa "A matsayi na na ɗan dimokiraɗiyya, ba na tilasta wa ’ya’yan na ra’ayi a kan abubuwa da suka shafi irin wannan lamarin haka kuma bazan tilasta wa ’yan Najeriya ba."

    Atiku ya jaddada cewa ra’ayin ɗansa ba zai sa shi canza manufarsa wajen aiki domin kawo ingantacciyar shugabanci ba.

    Abba Atiku dai ya sanar da barinsa PDP zuwa APC a ranar Alhamis, yayin wata ziyara da ya kai ofishin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan ƙasa, Sanata Barau Jibril.

    A jawabin nasa, Abba ya bayyana cewa dalilin sauya sheƙarsa shi ne sha’awarsa ga salon shugabanci da jajircewar Sanata Barau.

    Abba Atiku ya ce zai yi aiki tare da Sanata Barau domin ganin an sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a 2027.

    “Don haka zan yi aiki da Sanata Barau domin tabbatar da nasarar sake zaɓen Shugaba Tinubu a karo na biyu,” in ji shi, kamar yadda Sanata Barau ya wallafa a shafinsa na X.

    Atiku ya kuma ce abin da ya fi damunsa shi ne rashin kyakkyawan shugabanci na APC da kuma matsin tattalin arziki da zamantakewa da jam’iyyar ta jefa ’yan Najeriya a ciki inda ya ce zai ci gaba da aiki tare da masu kishin ƙasa domin samar da ingantacciyar shugabanci ga al’umma.

  4. Abin da ya sa aka binne Sardauna a Kaduna maimakon Sokoto

    A daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara kan cika shekara 60 da juyin mulkin soji na farko a Najeriya, wanda ya yi sanadiyar kifar da gwamnatin jamhuriya ta farko, wasu na ci gaba da tattaunawa kan tabon da matsalar ta haifar.

    Juyin mulkin ne ya yi sanadiyar mutuwar fitattun ƴansiyasa irin su Firaministan Najeriya na wancan lokaci Abubakar Tafawa Ɓalewa da Firimiyan Arewa Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto da takwaransa na Yamma Ladoke Akintola da sauransu.

    A yunƙurin juyin mulkin, wanda aka yi a ranar 15 ga watan Janairun shekarar 1966, wasu hafoshin sojin Najeriya ne suka yi yunƙurin juyin mulki, wanda shi ne na farko da aka fara samu bayan samun ƴancin kai.

    Baya ga manyan 'yan siyasa, juyin mulkin ya kuma rutsa da manyan jami'an sojin Najeriya.

  5. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Juma'a da Hausawa ke yi wa kirari da Hajji babbar rana.

    Abdullahi Diginza da Aisha Babangida ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Kuna iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafa a shafukanmu na sada zumunta.