Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Lahadi 01/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Lahadi 01/03/2026

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Hotunan ɓarnar da hare-haren Iran suka yi kan sansanonin sojin Amurka

    Hotuna na ci gaba da bayyana na yadda baƙin hayaƙi ke tashi bayan harin ramuwar gayyar Iran kan sansanonin sojin Amurka da ke Gabas ta Tsakiya.

    An ɗauki wasu daga cikin hotunan cikin dare, wasu kuma da safe a ƙasashen Bahrain da Haɗaɗdiyar Daular Larabawa.

  2. Harin Iran ya lalata wani gini a birnin Tel Aviv na Isra'ila

    Harin makami mai linzamin Iran ya lalata wani gida a tsakiyar Tel Aviv, babban birnin Isra'ila.

    Rahotonni daga ƙasar sun ce harin ya yi sanadin mutuwa mace guda, wadda ita ce mutuwa da farko da aka bayar da rahotonta a Isra'ila tun bayan fara wannan yaƙi.

    Isra'ila ta kakkaɓo kusan duka makaman linzami da Iran ta harba cikinta.

    Amma duk da haka wasu sun samu faɗawa ciki, musamman bayan tarwatsewa a sama.

  3. Iraƙi ta ayyana makokin kwana uku bayan kisan Khamenei

    Gwamnatin ƙasar Iraƙi ta ayyana makokin kwana uku a fadin ƙasar domin nuna alhini kan kisan jagoran addainin Iran Ayatollah Ali Khamenei.

    Cikin wata sanarwar da gwamnatin ƙasar ta fitar, ta aike da saƙon jaje ga al'ummar Iran, kan kisan jagoran addinin ƙasar, wadda ta bayyana da ''aikin takalar faɗa''.

  4. Dubban Iraniyawa na jimamin mutuwar jagoran addinin ƙasar

    Dubban Iraniya sun taru a birnin Tehran domin yin alhinin mutuwar jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei da Amurka da Isra'ila suka kashe a hare-harensu.

    Tuni dai hukumomin ƙasar suka sanar da makokin kwanaki 40 a faɗin ƙasar

    Ayatollah Ali Khamenei na da farin jini da ƙarfin faɗa a ji a ƙasar Iran

    Ya shafe fiye da shekara 35 yana jan ragamar ƙasar, mai ƙarfin faɗa a ji a yankin Gabas ta Tsakiya.

  5. 'Jiragen Iran sun yi ruwan boma-bomai kan sansanonin sojin Amurka'

    Kamfanin dillancin labaran Iran, IRNA ya ce jiragen yaƙin ƙasar sun yi ruwan boma-bomai kan sansanonin sojin Amurka da ke yankin Gulf da yankin Kurdistan na Iraƙi.

    Dakarun sojin Iran sun ce jiragen yaƙin ƙasar sun samu nasarar kai munanan hare-hare kan sansanonin.

    Sojojin sun ƙara da cewa ''duka sansanonin maƙiya'' a yankin ba su gagari jiragen yaƙin mu ba.