Mutum 39 sun mutu a Khartoum na Sudan sakamakon zazzaɓin Denge
Likitoci a Sudan na ƙoƙarin yaƙi da yaɗuwar zazzaɓin Denge wanda sauro ke yaɗawa.
A Khartoum, cutar ta kashe mutum 39 yayin da wasu ɗaruruwa suka kamu da ita.
Asibitocin birnin da dama ba su aiki saboda yadda yaƙi tsakanin dakarun gwamnati da mayaƙan RSF ya ɗaiɗaita su.
Ƙungiyar likitocin ƙasar ta ce mata da ƙananan yara na cikin waɗanda suka fi kamuwa da zazzaɓin na Denge a ƙasar.