Ƙasashen Sahel sun ƙaddamar da tutar ƙawance
Gamayyar ƙasashen Sahel da suka haɗa da Mali da Burkina Faso da Nijar sun ƙaddamar da tutar ƙawancen ƙasashen a birnin Bamako na Mali.
Wannan matakin ya biyo bayan amincewar da shugabannin ƙasashen ƙungiyar suka yi a ranar 22 ga watan Fabrairu.
An gabatar da tutar ce a wajen wani taro na ministocin ƙungiyar da aka kammala a yau Lahadi 23 ga wannan wata da muke cikin.
Ministocin na AES ne suka ƙaddamar da tutar mai launin kore da kuma tambarin ƙungiyar a tsakiyarta.