Sojojin Syria sun tsananta hare-hare a yankin Aleppo

Asalin hoton, AFP
Sojojin Syria sun tsananta hare-haren da suke yi a wasu sassan Aleppo, a yayin da suke ci gaba da gwabza faɗa da mayaƙan Ƙurɗawa.
An shiga kwana na uku ke nan da ake faɗa a birnin, tsakanin dakarun gwamnati da SDF. Dubban mutane sun rasa matsugunansu, kuma sojoji na ci gaba da kira ga fararen hula su fice daga wasu yankuna.
Har yanzu ƙungiyar SDF ce ke iko da yankuna da dama na arewa maso gabashin Syria, kuma sun ki amincewa su haɗe da gwamnatin ƙasar da ke amfani da tsarin musulunci.
Wata mazauniyar birnin kenan ta ce komai ya lalace, akwai mutane dayawa da suka so su tsere, amma suna fita aka soma harbi, dole suka koma gida.


















