Ministocin ƙasashen turai sun buƙaci a kai wa fararen hula ɗauki a Gaza

Asalin hoton, Getty Images
Ministocin kasashe 10 ciki har da Faransa, da Birtaniya, Japan da Canada sun yi gargadi kan mummunan halin jin kai da ake fama da shi a Gaza.
A sanarwar hadin gwiwa da suka fitar, sun yi maraba da kawo karshen yakin Gaza, amma sun ce yana da muhimmanci kar a manta da halin da farar hula ke ciki.
Kididdiga ta baya-bayan nan da aka fitar, ta nuna sama da Falasdinawa miliyan 1 ne ke tsananin bukatar wurin zama a daidai lokacin da ake fama da tsananin sanyi a Gaza.
Sannan rashin wuri mai tsafta ya bar dubban iyalai cikin hadarin ambaliya. Wannan kira na zuwa ne bayan kiran da kungiyoyin kasashe 25 da ke aiki a Gaza suka, na haramta musu gudanar da aiki a can sakamakon rashin cika sharuddan da ke cikin sabuwar rijistar da Isra'ila ta fitar.

















