Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 07/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 07/03/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. 'Iran ta sake kai hari sansanin sojin Amurka a Bahrain'

    Dakarun juyin juya halin Iran, IGRC sun ce sun kai harin ''manyan makamai'' masu linzami kan sansanin sojin Amurka da ke Bahrain.

    IRGC ta ce ta kai harin ne a matsayin martani ga wasu rahotanni da ba a tabbatar da su ba na cewa Amurka ta kai hari a wata cibiyar tace ruwa sha a wani tsibiri da ke mashigin Hormuz.

    "A matsayin martani ga harin da Amurka ta kai daga sansanin Juffair a kan tashar Qeshm, wannan sansanin na Amurka ya fuskanci mummunan hari daga rundunar IGRC'', a cewar wata sanarwa da IGRC ta fitar ta hanyar kafar yaɗa labaran Fasrna mai alaƙa da IGRC.

    A halin da ake ciki kuma, ana jin ƙarar sautin na'urorin ankararwa a Bahrain, inda ma'aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar ta buƙaci 'yan ƙasar da mazauna yankin su nufi wani wurin ɓuya mai aminci.

    A cikin 'yan mintoci da suka gabata ne ma'aikatar cikin gidan Bahrain ta wallafa a shafinta na X cewa an samu tashin gobara da ƙonewar wasu gine-gine a Manama, babban birnin Bahrain, inda ta ce jami'an kashe gobara na ƙoƙarin kashe wutar.

  2. Amurka ta nutsar da jiragen ruwan Iran 42 - Trump

    Shugaba Trump na Amaurka ya ce kasarsa na yin ''ƙoƙari'' a yaƙin Iran.

    Yayin da yake zantawa da manema labari a Florida ya ce a cikin kwana uku Amurka ta nutsar da jiragen ruwan Iran 42 a cikin teku.

    Shugaba Trump ya ce zai kai wa iyalan sojojin ƙasar da suka mutu a yaƙin Iran ɗin ziyarar ta'aziyya.

    Ya ce dukansu sun zama ''manyan jaruman ƙasarmu'', waɗanda za su dawo gida daga Iran a wani yanayi na daban.

    Ya ci gaba da cewa Amurka za yi duk mai yiwuwa don ganin mutuwar sojojinta ya ''taƙaita''.

  3. Dakarun juyin juya halin Iran sun ce sun kai wa Kurɗawan Iraƙi hari

    Dakarun juyin juya halin Iran, sun ce sun kai hari kan ƙungiyar ƴan'awaren Iraƙi da ke yankin Kurdistan mai ƙarya-ƙwaryan yanci.

    Cikin wata sanarwar da dakarun suka fitar, sun ce kai kai hari wurare uku a yankin da asubahin ranar Asabar.

    Rundunar juyin juya halin ta kuma gargaɗi duka wata ƙungiya kan yunƙurin shiga Iran.

    Dakarun sun ce sun yi amfani da jirgi maras matuƙi wajen kai wa wani jirgin dakon mai - ta suka bayyana da kadarar Amurka - hari a yankin Gulf.

    Hare-harenna Kurdistan na zuwa ne a daidai lokacin da ake yaɗa labarin cewa Amurka za ta yi amfani da mayaƙan Kurɗawan da ke arewacin Iraƙi wajen kai wa Iran hari.

  4. 'Hare-haren Isra'ila sun kashe aƙalla mutum 300 a Lebanon'

    Ma'aikatar lafiyar Lebanon ta ce hare-haren Isra'ila a ƙasar sun kashe kusan mutum 300 tun bayan fara yaƙi da hezbollah a ranar Litinin.

    Hukumar lafiyar ta ce fiye da mutum 1,000 ne suka jikkata sakamakon hare-haren.

    A gabashin Lebanon - inda rundunar sojojn Isra'ila IDFta ce tana aikin gano gawar wani sojan samanta da ya jima da ɓacewa mai suna Ron Arad - an kashe mutum 40 tare da raunata 41.

    Ministan tsaron Isra'ila Israel Katz, ya gargadi shugaban Lebanon, Joseph Aoun, cewa ƙasarsa za ta ''ɗanɗana kuɗarta'' idan ba ta iya ƙwace makaman Hezbollah ba.

  5. Trump ya gargaɗi Iran kan fuskantar sabbin hare-hare

    Shugaba Trump na Amurka ya gargaɗi Iran cewa za ta fuskanci ''mummunan hari'' a yau, tare da yin barazanar cewa Amurka ta za ta faɗada hare-harenta a ƙasar zuwa sabbin wurare da nufin abin da ya kira ''kammala wargaza ƙasar''.

    Mista Trump ya kuma yi zolaya ga afuwar da Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya nema ga maƙwabtan Iran saboda hare-haren da ƙasarsa ta kai musu a tsawon makon da ya wuce.

    Shugaban na Amurka ya bayyana alƙawarin daina kai wa maƙwabtan Iran hari da Mista Pezeshkian ya yi - muddin ba a ƙara kai mata hari daga cikin su ba - a matsayin miƙa wuya.

    Jim kaɗan bayan jawabin Mista Pezeshkian ne dai Qatar ta sanar da daƙile harin makami mai linzami, yayin da ita ma UAE ta sanar da kakkaɓo wasu makamai masu linzami 15.

  6. Manyan malaman Iran sun yi kiran gagauta zaɓar sabon jagoran addinin ƙasar

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun cewa wasu manyan malaman ƙasar biyu masu ƙarfin faɗa-a-ji sun yi kiran gaggauta zaɓar sabon jagoran addinin ƙasar domin daidaita al'amuran ƙasar mai fama da hare-haren Amurka da Isra'ila.

    Tun bayan kisan Ayatollah Ali Khamenei, wata majalisa mai mambobi uku ce ke jagorantar ƙasar, har zuwa lokacin da za a zaɓi sabon jagoran addinin.

    Wasu malaman sun ce ya kamata a gaggauta zaɓen domin daidaituwar al'amura a ƙasar.

    Shugaba Trump ya buƙaci a sanya Amurka cikin masu zaɓen sabon jagoran addinin, wani abu da Tehran ɗin ta yi watsi da shi.

  7. 'Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga 45 a Katsina'

    Jami'ai a arewacin Najeriya na cewa sojojin ƙasar sun kashe ƴanbindiga 45 da suka kai hari wani ƙauye a jihar Katsina da ke arewacin ƙasar.

    Lamarin ya faru ne ranar Juma'a da maraice kamar yadda hukumomin jihar suka tabbatar.

    Rahotonni sun ce tun da farko ƴanbindigar waɗanda suka taso daga jihar Zamfara mai makwabtaka, sun kai hari ƙauyen Alhazawa na ƙaramar hukumar Danmusa a ranar Alhamis domin satar shanu.

    To sai dai mazauna garin sun nuna turjiya inda suka kashe huɗu daga cikin maharan.

    Kwana guda bayan hakan ne kuma ƴanbindiga suka sake taruwa da nufin ɗaukar fansa kan mazauna ƙauyen, inda suka ci karo da sojoji a kan hanyar tasu, lamarin da ya haifar da musayar wuta tsakani.

    Bayanai na cewa an kashe sojojin ƙasar uku a lokacin gumurzun.

  8. Kamfanin mai na Amurka na kwashe ma'aikatansa daga Iraƙi

    Kamfanonin mai na ƙasashen waje a yankin Gabas ta Tsakiya sun fara kwashe ma'aikatansu daga rijiyoyin haƙar mai a Iraƙi.

    Hotnan da kamfani dillancin labarai na Reuters ya wallafa sun nuna yadda ma'aikatan ke fita daga Iraƙi ta kan iyakar Kuwait.

    wani maigadin kamfanin haƙar mai na Halliburton mallakin Amurka, ya shaida wa Reuters cewa ''ma'aikatan kamfanin na ficewa daga ƙasar ne zuwa Kuwait saboda dailai na tsaro''.

    ''Daga can ne kuma za su yanke shawarar inda ya kamata su tafi'', in ji shi.

    An riƙa kai hare-hare kan cibiyoyin man fetur a yankin Gabas ta Tsakiya tun bayan fara yaƙin Iran tsawon mako guda.

  9. An raunata sojojin Ghana biyu a kudancin Lebanon

    Hukumomin ƙasar Ghana sun shigar da ƙorafi a hukumance gaban babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, bayan da wani hari a kudancin Lebanon ya ji wa sojojinta biyu - da ake aikin wanzan da zaman lafiya - munanan raunkuna.

    Ministan harkokin wajen ƙasar, Samuel Okudzeto Ablakwa ya ce gwamnati na son a gudanar da ''cikakekn bincike ba tare da son rai ba game da harin'', wanda ya ce ya saɓa wa dokokin duniya, kuma ya zama laifin yaƙi''.

    Sojojin Ghana na aiki da rundunar Majalisar Dinkin Duniya a Lebanon (UNIFIL), wadda aka kai domin sanya idanu a kan iyakar Isra'ila da Lebanon.

    Rundunar sojin Ghana ta ce, an kai wa bataliyar sojojin Ghana hari da makamai mai linzami a ranar Juma'a da maraice.

    Kawo yanzu ba a son wanda ya kai harin ba.

  10. An ga wuta da baƙin hayaƙi na tashi a filin jirgin saman Iran

    Sabbin hotunan da ke fitowa daga Iran na nuna yadda hayaƙi ya turnuƙe saman filin jirgin Mehrabad a birnin Tehran.

    An ɗauki hotunan daga bidiyoyin da ke yawo a shafukan sada zumunta, kuma kamfanin dillancin labarai na Reuters ya tabbatar da wurin da aka ɗauki bidiyoyin.

    Sai dai kamfanin ya ce bai iya tantance ranar da aka ɗauki hotunan ba, sai dai babu wani tsohon bidiyo da ya yi kama da shi a baya.

    Tun da farko shaidu sun bayar da rahoton jin ƙarar manyan abubuwan fashewa a filin jirgin mafi cunkuson mutane.

  11. Filin jirgin Dubai ya koma aiki 'kaɗan-kaɗan'

    Babban filin jirgin sama na Dubai ya ce ya koma ''aiki kaɗan-kaɗan'', inda wasu jirage ƙalilan suka tashi daga filin.

    Tun da farko a yau hukumar kula da filin jirgin ya sanar da dakatar da aiki.

    Sai har yanzu ana ta sauya wa jirage lokacin tashi, don haka ake bai wa fasinjoji shawarar kada su je filin jirgin, har sai kamfanin jirgin da za su hau ya tuntuɓe su don tabbatar musu da tashin jirginsu.

  12. Sojojin Isra'ila sun ce sun kai sabbin hare-hare a Tehran da Isfahan

    Rundunar sojin Isra'ila, IDF ta ce ta fara kai abin da ta kira manyan hare-hare kan wasu muhimman wurare a biranen Tehran da Isfahan.

    IDF ta bayyana hakan ne a shafinta na Telegram.

  13. Mun kai wa wani jirgin dakon mai hari a mashigar Hormuz - Iran

    Rundunar dakarun juyin juya halin Iran (IRGC) ta ce ta kai hari kan wani jirgin dakon mai na wata ƙasar yankin Gulf da ya ratsa ta mashigar Hormuz.

    Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafinta na Telegram, ta ce jirginta maras matuƙi ne ya kai wa jirgin dakon man hari, saboda ''watsi da gargaɗin bi ta mashigar da runudunar IRGC ta sha yi''.

    Rundunar IRGC ta ƙara da cewa ba za ta bari jiragen dakon mai da na kasuwanci ''masu ƙawance da ''ƙasashen da muke faɗa da su'' su bi ta mashigar ba.

    Zirin Hormuz na ɗaya daga cikin hanyoyin jigilar makamashi mafiya muhimmanci a duniya, inda kusan kashi ɗaya cikin biyar na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta wurin zuwa kasuwanni.

    Yaƙin da ake yi a Iran ya haifar da nakasu ga harkar safarar mai a yankin Gulf, bayan da gwamnatin Iran ta yi baranazar ƙona duk wani jirgin dakon mai da ya yi yunƙurin wucewa ta wurin.

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce ''idan ta kama'' sojojin ruwan Amurka za su riƙa yi wa jiragen rakiya don su wuce ta wurin.

  14. Iran ta nemi afuwar ƙasashe maƙwabta

    Shugabna ƙasar Iran,Masoud Pezeshkian ya nemi afuwar ƙasashe maƙwabtan ƙasar kan hare-haren da ƙasarsa ta kai musu.

    Cikin wani saƙon bidiyo da aka yaɗa ta gidan talbijin na ƙasar, Mista Pezeshkian ya ce ''ya zama wajibi mu nemi wannan afuwa na ƙasashen da muka kai wa hari''.

    "Ba mu da niyyar far wa maƙawambtanmu''.

    Tun bayan da Isra'ila da Amurka suka ƙaddamar da hare-hare kan Iran tare da kashe jagoran addinin ƙasar, Iran ta mayar da martani ta hanyar ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.

    Pezeshkian ya ƙara da cewa gwamnatin ƙasar ta bai wa sojojin ƙasar umarnin ''daga yanzu kada a sake kai wa wata ƙasa maƙwabciyarmu hari, in ba ita ta fara kawo mana harin ba.''

    “Ga waɗanda ke tunanin za su yi amfani da wannan lokaci da muke ciki don kai wa Iran hari, su sani ba za mu ƙyale ba, kuma goyon bayan Isra'ila ko Amurka ba ahnya ce ta girmama ƴanci ba'', in ji shi.

  15. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannna rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannann lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki, musamman labaran yaƙin Iran da Amurka.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.