Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 16/12/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 16/12/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Farashin kayan abinci ya tashi sakamakon bukukuwan ƙarshen shekara - NBS

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar ƙididdigar ƙasa ta Najeriya (NBS) ta bayyana cewa farashin kayan abinci ya hau ta dalilin bukukuwan karshen shekara da kuma matsalolin tsaro a watan Nuwamba 2025.

    Wannan ya sa matsakaicin hauhawar farashin kaya a wata-wata ya kai kashi 1.22 cikin 100, mafi girma cikin watanni hudu, inda masana ke hasashen irin wannan yanayi zai ci gaba a watan Disamba.

    Haka zalika, hauhawar farashin abinci a wata-wata ya kai kashi 1.13 cikin dari, mafi girma cikin watanni uku, sakamakon ƙaruwar farashin wasu kayan abinci da ake amfani da su a kowace rana.

    Wannan ya nuna yadda buƙatun ƙarshen shekara da matsalolin tsaro ke shafar rayuwar talakawa musamman wajen samun kayan abinci.

    Sai dai, NBS ta bayyana cewa, duk da tashin farashin wata-wata, matsakaicin hauhawar farashi na shekara-shekara ya ci gaba da raguwa na tsawon watanni takwas, daga kashi 16.05 cikin dari a watan Oktoba zuwa kashi 14.45 cikin 100 a watan Nuwamba.

    Wannan raguwa ta nuna cewa hauhawar farashin kaya gaba ɗaya yana raguwa a hankali duk da tashin farashin abinci a wasu lokuta.

    A bangaren abinci, NBS ta nuna cewa farashin abinci a shekara-shekara ya kai kashi 11.08 cikin 100 wanda ya ragu sosai idan aka kwatanta da kashi 39.93 cikin dari da aka samu a Nuwamba 2024.

    Amma a wata-wata, farashin abinci ya tashi da kashi 1.13 cikin 100, musamman farashin tumatir da dankalin da rogo da barkono da ƙwai da naman shanu da albasa da dai sauransu.

  2. An gano asalin ɗaya daga cikin ƴan bindigar da suka kashe mutum 15 a Bondi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomin Indiya sun ce ɗaya daga cikin yanbindigar da suka kashe mutum 15 a Bondi ranar Lahadi 'dan Indiya ne.

    Yansanda a kudancin jihar Telangana sun ce Sajid Akram 'dan Hyderabad ne da ya koma Australia shekaru 27 da suka gabata.

    Jami'ai a Australia na binciken abinda ya sa ƴan bindigar suka kwashe kusan wata 'daya a Philipphines, inda aka jima da samun ɓillar masu iƙirarin jihadi.

    Ana cigaba da matsawa hukumomin tsaro lamba anan inda suka yi bayanin alaƙar da ke tsakanin yan bindigar da ƙungiyar masu iƙirarin jihadi.

    Yan sandan Australia sun harbe ɗaya daga cikin ƴanbindigar yayin da rahotanni suka ce matashin ya farfado daga dogon suma a asibiti.

  3. Afcon 2025: ƴan wasan da aka gayyata buga gasar kofin Afirka

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Za a fara gasar cin kofin nahiyar Afirka karo na 35 a Morocco daga 21 ga watan Disambar 2025 zuwa 18 ga watan Janairun 2026.

    Tawagar Ivory Coast ce mai rike da kofin, bayan da ta doke Najeriya 2-1 ta lashe kofin a 2023 da ta gudanar da wasannin, kuma karo na uku da ta ɗauka.

    Kasa 24 za su kece raini da aka amince kowacce ta gayyaci ƴan wasa 28 da za su buga mata gasar da za a fara a cikin watan Disamba.

    Tun daga Alhamis 11 ga watan Disamba aka rufe karɓar sunayen ƴan wasan da za su wakilci kowacce tawaga - sannan an umarci ƙungiyoyi su bar ƴan ƙwallon da za su je Afcon tun daga ranar Litinin 15 ga watan Disamba.

    Ga jerin ƴan wasa da kowacce tawaga ta gayyata, domin buga gasar cin kofin Afirka da za a yi a Morocco a 2025/26.

  4. Ganduje ya janye ƙudirin kafa rundunar Hisba Fisabilillah a Kano

    ..

    Asalin hoton, Ganduje/Facebook

    Tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya sanar da janye yunƙurinsa na kafa rundunar ƴan sakai da ya kira da Hisba Fisabilillah.

    A wata sanarwa da shugaban kwmaitin na kafa Hisba a Kano ƙarƙashin Ganduje, Baffa Babba Ɗan Agundi ya fitar ranar Talata, Ganduje ya ce janyewar ta faru ne bayan ganawa da masu ruwa da tsaki daga ƙananan hukumomin jihar guda 44 na jihar.

    .Sanarwar ta ce an yanke shawarar sauya matsayar ne sakamakon martani da jama'a suka yi ta yi da kuma damuwa da ruɗu da al'amari ya janyo.

    ‘’Masu ruwa da tsakin sun cimma matsayar cewa mun fasa kafa rundunar domin bai wa gwamnatin jiha ta waiwayi korar ma'aikan Hisba da ta yi ta kuma warware matsalar ta hanyar tattaunawa," in ji sanarwar.

  5. Mece ce lambar TIN da ake son duk mai asusun banki ya mallaka?

    ..

    Asalin hoton, FIRS/WEB SITE

    Da alama ƴan Najeriya sun shiga ruɗu dangane da rashin sanin abin da zai faru da su daga ranar 1 ga watan Janairun 2025 lokacin da sabuwar dokar haraji ta ƙasar za ta fara aiki.

    Matakin farko na wannan haraji shi ne cewa dole ne duk ɗan Najeriya da ke hulɗa da asusun banki ya mallaki lambar TIN wadda ta nan ne za a san wane ne ya kamata yi biya harajin sannan kuma nawa zai biya.

    Irin wannan ruɗani dai ya fara ne a watan Satumbar 2025 ɗin nan lokacin da gwamnatin ƙasar ta fitar da sanarwar wajabcin mallakar lambobin na TIN ga ƴan ƙasa domin samun damar amfani da asusunsu na bankunan a nan gaba.

    Shugaban kwamitin shugaban ƙasa kan gyaran fuska ga sha'anin kuɗi da haraji na Najeriya, Taiwo Oyedele ne ya sanar da hakan da farko to amma daga baya sai ya fayyace abin da yake nufi bayan al'amarin ya tayar da ƙura.

    "Wajabcin mallakar wannan lambar ta taƙaitu ne ga mutane da kamfanonin da ya kamata su biya haraji - ba ta shafi ƴan Najeriyar da abin da suke samu bai kai a cire musu haraji daga ciki ba," in ji Oyedele.

    Shin mece ce ita wannan lambar? Kuma yaya ake samun ta? BBC ta yi nazari kamar haka:

  6. Ɗan ƙunar-baƙin-wake ya kashe sojojin Najeriya biyar a Borno

    Sojojin Najeriya riƙe da bindigogi a lokacin atisaye.

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Sojojin Najeriya riƙe da bindigogi a lokacin atisaye.

    Wani ɗan ƙunar baƙin wake ya tayar da bam inda ya kashe sojoji guda biyar, a garin Puka da ke yankin ƙaramar hukumar Gwoza a jihar Borno.

    Kwamishinan watsa labarai na jihar wanda ya tabbatar wa da BBC faruwar al'amarin ya ce abin ya faru ne ranar Lahadi, inda ake kyautata zaton ɗan ƙunar baƙin waken ɗan ƙungiyar Boko Haram ne wanda ya fito daga maɓoyarsa da ke kan duwatsun Mandara.

    Ɗan ƙunar Baƙin waken ya yi shigar burtu a matsayin matafiyi inda ya tayar da bam ɗin a kusa da sojoji a wani shingensu kuma nan take ya kashe sojojin biyar.

    Har kawo yanzu dai rundunar sojin Najeriya ba ta komai ba dangane da wannan kisan da aka yi wa sojojinta.

    A baya-bayan nan ne sabon ministan tsaron Najeriya, Manjo Janar Christopher Musa ya yi umarnin kwashe sojoji daga shingaye da ke kan tituna domin mayar da su zuwa dazuka saboda su tunkari ƴan ta'adda.

  7. Ruwan sama ya ƙara tsananta halin da mutanen Gaza ke ciki

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Jami'an aikin agaji sun ce ruwan sama mai ƙarfi ya ƙara haifar da tsanani a Gaza, inda ya yi awon gaba da dubban tentina tare da rushe gine-gine da yaƙin Isra'ila na shekaru biyiu ya lalata.

    Rahotanni sun ce wani Bafalasɗine ya mutu yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon rushewar wani ɓangaren rukunin wasu gidaje ranar Talata.

    Yoyon ruwan sama cikin asibitin Al Shifa ya dakatar da ayyukan jinya.

    Wani jami'in agajin hukumar yan gudun hujira ta Norway ya shaidawa BBC cewar Falasdinawan da yakin Isra'ila ya raba da muhallansu na halin ni 'ya su.

  8. Tsohon shugaban alƙalan Najeriya Ibrahim Tanko ya rasu

    ...

    Asalin hoton, Twitter/@NGRPresident

    An sanar da rasuwar tsohon shugaban alƙalan Najeriya, mai shari’a Ibrahim Tanko Muhammad, yana da shekaru 71 a duniya.

    Wata sanarwa da gwamnatin jihar Bauchi ta fitar, wadda ta samu sa hannun Mukhtar Gidado, mai magana da yawun gwamnan jihar Bala Mohammed, ta ce "Tanko ya rasu ne yau a ƙasar Saudiyya bayan fama da doguwar jinya."

    Tanko Muhammad, ɗan asalin jihar Bauchi ya riƙe muƙamin shugaban alƙalan Najeriya ne daga shekarar 2019 zuwa 2022 ƙarƙashin tsohon shugaban Najeriya, marigayi Muhammadu Buhari.

    Haka kuma ya taɓa zama alƙalin Babbar Kotu, da Kotun Ɗaukaka ƙara da kuma Kotun Ƙoli ta Najeriya.

    Gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya bayyana rasuwar mai shari'a Ibrahim Tanko a matsayin "babbar hasara ga Najeriya baki daya".

  9. Mutum miliyan 17 na fuskantar matsananciyar yunwa a Afghanistan - WFP

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da suka haɗa da shirin samar da abinci ta duniya WFP sun yi gargaɗin yanayin da ake ciki a Afghanistan ya munana, inda sama da mutum miliyan goma sha bakwai suke fuskantar matsananciyar yunwa a lokacin hunturu.

    Wani babban jami'n hukumar ya ce tawagarsu ta shaida yadda iyalai ke tsallake cin abinci na tsawon kwanaki, sannan akwai damuwa game da yadda yara ke rasa abinci mai gina jiki.

    Hukumar ta ce tana buƙatar miliyoyin daloli don ciyar da mutanen da suka fi rauni a Afghanistan .

    Yunwar ta yi tsanani ne sakamakon komawar yan gudun hijira daga Iran da Pakistan da yawansu ya kai miliyan biyu da rabi.

    Afghanistan na dab da shiga tsananin yanayin hunturu, rabin ƙasar ya yi fama da fari, rashin ayyukan yi da matsalar tattalin arziki ta taɓa rayuwar al'umma.

  10. Majalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatar

    ...

    Asalin hoton, Nigeria Senate

    Majalisar dattawa ta amince da naɗin mutum uku na farko da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar mata domin tantancewa a matsayin jakadun Najeriya a ƙasashen waje.

    Sabbin jakadun da majalisar ta amince da naɗin nasu su ne Aminu Muhammad Dalhatu daga Jihar Jigawa, Lateef Kayode Kolawole Are daga Jihar Ogun, da kuma Emmanuel Ayodele Oke, CFR, daga Jihar Oyo.

    Majalisar ta amince da naɗin ne bayan la’akari da rahoton kwamitin majalisar dattawa kan harkokin waje, wanda ya gudanar da tantancewar waɗanda aka gabatar a makon da ya gabata.

    Sai dai har yanzu akwai ragowar wasu 64 da shugaba Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa, waɗanda aka tantance amma ba a kai ga tabbatar da naɗin nasu ba.

    Shugaba Tinubu ya tura sunayen waɗannan jakadu uku ne a ranar 26 ga Nuwamba.

    Wannan shine jerin sunaye na farko na jakadu da Shugaban ƙasa ya miƙa wa Majalisar Dattawa tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023.

  11. Ƴan tawayen ƙungiyar M23 sun janye daga Uvira

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƴan tawayen ƙungiyar M23 sun janye daga birnin Uvira, in ji sanarwar da Corneille Nangaa ya fitar a ranar Talata.

    Nangaa, wanda shi ne kwamandan ƙungiyar Fleuve Congo Alliance (AFC), wacce ke ɓangaren ƙungiyar M23, ya bayyana cewa matakin janyewar wani abu ne na gina amana, domin bai wa tattaunawar zaman lafiya ta Doha damar samun nasara.

    Mutanen Uvira sun shaida wa BBC cewa burinsu kawai shine zaman lafiya mai ɗorewa da kuma a daina harbin bindiga

    Wannan janyewar ta biyo bayan shigar ƴan tawayen AFC/M23 birnin Uvira a ranar Laraba, inda suka ƙwace cikakken iko da garin bayan kai hari daga Kamanyola, wanda ke kilomita 75 daga arewacin birnin.

    Ƙungiyoyin AFC/M23 sun rattaɓa hannu kan yarjejeniyar tsarin ayyuka da gwamnatin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo a ranar 15 ga Nuwamba, wadda ta haɗa da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta.

  12. MDD ta nemi a saki mutum 10,000 da aka tsare ba bisa ƙa’ida ba a Eritrea

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Dinkin Duniya ta yi maraba da sakin ƴan Eritrean 13 da aka tsare kusan shekaru 18 ba tare da shari’a ba, inda ta bayyana hakan a matsayin ci gaba mai kyau, sannan ta yi kira ga hukumomin ƙasar da su saki duk sauran mutanen da aka tsare ba bisa ka’ida ba.

    A wata sanarwa da aka fitar, MDD ta buƙaci Eritrea da ta saki duk wadanda suka rage a kurkuku ba tare da sharaɗi ba, ciki har da tsoffin manyan jami’an gwamnati da ak

    MDD ta kiyasta cewa fiye da mutane 10,000 ne a ke tsare da su ba bisa ka’ida ba a Eritrea, ciki har da ‘yan siyasa da ‘yan jarida da shugabannin addini da dalibai.a kama a shekarar 2001 saboda kira na sauye-sauye a harkokin siyasa da shugabanci.

    Gwamnatin Eritrea ta saki mutum 13 ɗin ne a ranar 4 ga Disamba, waɗanda suka haɗa da ‘yan kasuwa da jami’an ‘yan sanda da sauran ƙwararru da suke tsare a kurkukun soji na Mai Serwa kusan shekaru ashirin.

    Haka kuma, majiyoyi daga cikin ƙasar da waje sun bayyana wa BBC cewa hukumomin sun kuma saki mabiya cocin da aka haramta guda 98, da dama daga cikinsu suna tsare tsawon shekaru.

  13. Ƴansanda sun ce za su ci gaba da kama masu gilashin mota mai duhu

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Ƴansandan Najeriya sun sanar da cewa za su ci gaba da tilasta bin dokar mallakar lasisin amfani da gilashin mota mai duhu ko kuma su ci gaba da kame daga 2 ga Janairu 2026, abin da ya janyo suka daga ƙungiyar lauyoyin Najeriya (NBA), wadda ta bayyana matakin a matsayin saɓa wa hukuncin kotu da kuma tauye doka.

    Wannan sanarwa ta fito ne daga CSP Benjamin Hundeyin, jami’in hulɗa da jama’a na hukumar ƴan Sanda, a ranar 15 ga Disamba 2025.

    NBA ta bayyana cewa matakin ƴansandan ya saɓawa hukuncin da kotu ta yanke inda ta dakatar da aiwatar da dokar har sai an gama shari’ar ƙarar ƴansandanda aka shigar a gabanta na ƙalubalantar halaccin dokar.

    Lauyoyi sun yi gargadi cewa wannan mataki zai ƙara nauyi ne ga talakawa, kuma zai iya jawo cin hanci da rashawa.

    Wannan lamarin ya fara ne a watan Afrilu 2025 lokacin da rundunar ƴansandan Najeriya ta shigo da dokar mallakar lasisin gilashin mota mai duhu, wacce ta bukaci ‘yan Najeriya su yi rijista ta intanet domin samun lasisi inda aka tsara fara aiwatar da dokar a ranar 1 ga Yuni 2025, daga baya aka ɗage zuwa 2 ga Oktoba saboda korafe-korafe da dama daga jama’a.

    NBA ta buƙaci ƴansandan da su dakatar da duk wani mataki na ci gaba da aiwatar da dokar har sai kotu ta yanke hukunci na ƙarshe.

  14. Mutum 8 sun mutu a hare-haren sojojin Amurka kan jiragen da ake zargi da safarar ƙwayoyi

    ...

    Asalin hoton, US Southern Command

    Sojojin Amurka sun ce sun kai hare-hare kan jiragen ruwa uku da ake zargi da safarar ƙwayoyi a Tekun Pasifik, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum takwas.

    Rundunar sojin kudancin Amurka ta wallafa faifan bidiyon hare-haren a shafukan sada zumunta, inda ta ce jiragen na tafiya ne ta hanyoyin da aka san ana safarar miyagun ƙwayoyi, kuma suna cikin ayyukan safarar kwayoyi.

    A cewar sojojin, sama da jiragen ruwa 20 a Tekun Pasifik da na Caribbean aka kai wa hare-hare a ‘yan watannin nan, inda aƙalla mutum 90 suka rasa rayukansu.

    Wannan wani ɓangare ne na tsaurara matakan da shugaba Donald Trump ke ɗauka kan ƙungiyoyin da yake zargi da safarar kwayoyi zuwa yankin.

    Sai dai wasu masana sun ce waɗannan hare-hare na iya saɓawa dokokin yaƙi na kasa da kasa.

    Harin farko da aka kai a ranar 2 ga Satumba ya jawo ce-ce-ku-ce musamman, domin an ce an kai hari sau biyu inda waɗanda suka tsira daga harin farko aka kashe su a na biyu.

    Wasu kwararrun masana shari’a sun shaida wa BBC Verify cewa harin na biyu da sojojin Amurka suka kai kan wani jirgin ruwa mai safarar ƙwayoyi da ake zargin na Venezuela ne, mai yiyuwa ya saɓa doka, kuma ana iya ɗaukarsa a matsayin kisan gilla ba tare da shari’a ba a karkashin dokar kasa da kasa.

    A martaninta, Fadar White House ta ce matakan da aka ɗauka sun yi daidai da dokokin yaƙi, domin kare Amurka daga kungiyoyin safarar kwayoyi da take zargin suna kokarin “shigar da guba zuwa kasar da lalata rayukan ‘yan ƙasar.

  15. Gobara ta laƙume kasuwar katako a Gombe

    ...

    Asalin hoton, Gombe state government

    Wata gobara ta tashi a kasuwar katako da ke yankin tashar jirgin ƙasa a birnin Gombe, inda ta ƙone shaguna da kayayyaki masu yawa, lamarin da ya janyo asara mai tsanani ga ‘yan kasuwa da dama.

    Gobarar ta faru ne a daren Litinin, bayan ‘yan kasuwa sun rufe kasuwancinsu, kuma ta durƙusar da sana’o’in mutanen da ke dogaro da kasuwar wajen samun abin rayuwa.

    Gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana alhini da jimami matuƙa bisa faruwar lamarin.

    A cikin wata sanarwa da Darakta-Janar na harkokin yaɗa labarai na gwamnatin jihar, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi da juyayi ga al’ummar da abin ya shafa, tare da miƙa saƙon jaje ga dukkan ‘yan kasuwa da masu shagunan da gobarar ta rutsa da su.

    Sanarwar ta ce "Gwamna Inuwa ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa gwamnatin jihar na tare da su a wannan lokaci mai wahala, inda ya umarci hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar (SEMA) da sauran hukumomi masu alaƙa da su da su hanzarta bincike kan musabbabin gobarar, tare da kai tallafi da agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.

    Gwamnan ya kuma jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa wata cibiyar kwana-kwana ta zamani mai kayan aiki na ƙwarewa domin ƙarfafa kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

  16. Za mu ɗora a kan inda Buhari ya tsaya - Tinubu

    ...

    Asalin hoton, Tinubu/X

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ayyuka da manufofin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, inda ya ce za su ɗora a kan inda ya tsaya.

    Shugaba Tinubu ya faɗi hakan ne a ranar Litinin a Abuja, yayin ƙaddamar da littafin tarihin Buhari da Dr Charles Omole ya rubuta.

    Tinubu ya ce mafi girman girmamawa da za a yi wa Buhari ita ce ci gaba da ayyuakan shugabancinsa daga inda ya tsaya.

    Ya bayyana cewa littafin ya nuna tarihin Buhari cikin adalci, yana bayani kan nasarori da kuma kura-kurai, tare da ƙarfafa shugabanni na gaba su koyi darussa daga rayuwar marigayin.

    Shugaban ƙasar ya kuma waiwayi doguwar tafiyarsa ta siyasa tare da Buhari, inda ya bayyana shi "A matsayin ɗan’uwa da aboki da abokin tafiya a siyasa."

    Ya ce "Mun gina babbar haɗaka ta siyasa wadda ta kai ga nasarar zaben 2015, inda aka kayar da shugaban ƙasa mai ci a lokacin, lamarin da ya sauya yanayin siyasar Najeriya."

    Tinubu ya jaddada cewa haɗin kai a siyasa ba rauni ba ne, illa hikima wajen gina ƙasa.

    A wajen taron, gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya yabawa Shugaba Tinubu kan tsayawa tare da iyalan Buhari da kuma jihar Katsina, yana mai bayyana Buhari a matsayin mutum mai ladabi da kishin ƙasa da shugabanci nagari.

    Marubucin littafin, Dr Charles Omole, ya ce littafin ya tattaro tarihin rayuwar Buhari tun daga haihuwa har zuwa rasuwarsa, tare da shaidu daga mutanen da suka yi aiki tare da shi.

  17. Donald Trump ya kai BBC ƙara, yana neman diyyar dala biliyan 5

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya buƙaci BBC da ta biya shi biliyoyin daloli saboda zargin ɓata masa suna da ta yi a wata kotu da ke Florida.

    Trump ya buƙaci a biyashi diyyar dala biliyan biyar saboda sunan da aka ɓata masa a zarge-zarge biyu.

    An cire wasu sashe biyu a jawabin da Trump ya gabatar a ranar 6 ga watan Janairun 2021 a cikin wani shirin Panorama.

    Trump ya ce gyaran da aka yi wa jawabin nasa, ya nuna kamar yayi kira da a ɗauki doka a hannu, gabanin ɓarkewar rikicin da aka yi a ginin majalisar dokokin ƙasarsa a 2021.

    BBC dai ta nemi afuwarsa akan hakan to amma ta yi watsi da bukatarsa ta biyansa diyya.

  18. Wane zaɓi ya rage wa gwamnoni bayan kotun ƙoli ta bai wa Tinubu ikon tuɓe su?

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Tun bayan da kotun ƙoli ta bai wa shugaban Najeriya, Bola Tinubu ƙarfin ayyana dokar ta-ɓaci a kan jihohi da ma ikon tuɓe zaɓaɓɓen gwamna da ƴanmajalisa, ƴan Najeriya ke ta bayyana ɗarɗar dangane da ƴancin zaɓaɓɓun shugabanni a jihohi.

    A ranar Litinin ɗin da ta gabata ne dai Kotun Ƙolin Najeriyar ta yanke hukunci cewa shugaban ƙasa na da ikon dakatar da zaɓaɓɓen jami'in gwamnati a lokacin da aka ayyana dokar ta-ɓaci a wata jiha.

    Kwamitin alƙalai bakwai ne dai suka yanke hukuncin, inda shida daga ciki suka amince da matsayar kotun, yayin da alƙali guda ɗaya ya bayar da ra'ayi na daban.

  19. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu ci gaba daga inda muka tsaya a jiya na labaran kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a cikin Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.