Starmer na fuskantar matsin lamba ya yi murabus
Firaministan Biritaniya Sir Keir Starmer na fuskantar matsin lamba da ya yi murabus, sakamakon kashin da jam'iyyarsa ta sha a faɗin Birtaniya a zaɓen da aka gudanar a makon jiya.
Ƴan majalisar wakilai sama da saba'in ne suka yi kira gare shi da ya sauka daga mulki.
Wakilin BBC ya ce Birtaniya ta yi Firaminista huɗu a cikin shekaru huɗu da suka gabata. Yanzu kuma ga wani ya tsinci kansa a tsaka mai wuya; yayin da yan jam'iyyarsa ke tayar da ƙayar baya, kuma majalisar ministocinsa ta rabu kan ya tsaya ko ya tafi.
Manyan ministoci da dama sun buƙace shi da ya fitar da jadawalin saukarsa daga karagar mulki.
A jiya Litinin Sir Starmer ya dage cewa ba zai yi murabus ba, kuma zai yaƙi duk wani ƙalubale ga shugabancinsa.