Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Labarin wasanni daga 20 zuwa 26 ga watan Satumbar 2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Asabar 13 zuwa 19 ga watan Satumbar 2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Barcelona ta farfaɗo ta doke ƙungiyar Carzola, Oviedo

    Barcelona ta farfado daga baya ta kauce wa shan kunya a hannun daya daga cikin na karshen tebur a Laliga Real Oviedo, inda ta rama kwallo daya da mai masaukinta ta sa mata a raga har kuma ta kara biyu aka tashi 3-1.

    Miniti 33 da wasa Alberto Reina ya ribaci kuskuren mai tsaron ragar Barcelona Joan Garcia, ya daga ragar bakin ya sa Oviedo gaba, to amma bayan hutun rabin lokaci Barcelona ta ce ruwa ba sa'an kwando ba ne, inda 'yna wasanta Eric Garcia, da Robert Lewandowski da Ronald Araujo suka fitar da ita kunya da kwallo uku.

    Wannan nasara ta sa Barcelona ci gaba da wasa ba tare da an doke ta ba a wannan kakar ta bana.

    Tsohon danwasan kuma na tsakiya na Sifaniya Santi Cazorla mai shekara 40, ya shiga wasa tun da farkon take leda a karon farko a gasar ta La Liga ta bana a kungiyar.

    A 2003, ya bar Real Oviedo din kungiyar da ya fara yana yaro a dole saboda saboda matsalar kudi.

    Ya koma kungiyar a 2023, kuma a bara ya taimaka mata ta sake komawa babbar gasar ta Sifaniya a karon farko tun 2001.

    Barcelona ta ci gaba da zama ta biyu a tebur da maki 16 a wasa shida, inda maki biyu yake tsakaninta da Real Madrid ta daya.

    Ita kuwa Real Oviedo ta kasance ta 18 a teburin mai kungiyoyi 20, inda take da maki 3, Mallorca da Girona da take samansu suna da maki biyu kowacce.

  2. Ana nuna wa mata wariya a harkar ƙwallon ƙafa - Mai horda da Chelsea

    Mai horad da kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta mata Sonia Bompastor ta ce daya daga cikin tambayoyin da ake yawan yi mata wajen tantancewar daukar aiki ita ce ko za ta iya jagorantar babbar kungiya kuma tana mace uwa.

    Bompastor, wadda take da 'ya'ya hudu ta jagoranci Chelsea ta ci kofi uku a Ingila a baya.

    Da aka tambaye ta game da wani bincike da aka yi kwanan nan wanda ya gano cewa kashi 78 cikin dari na mata na fuskantar wariya a harkar wasan kwallon kafa, sai ta ce ba ta mamaki.

    ''Ka san tambayar farko da kowa yake yi min idan ina neman aikin kociya,'' in ji Bompastor mai shekara 45.

    "Zan gaya maka - 'kina ganin abu ne da zai yiwu ki kisance uwa mai 'ya'ya hudu kuma mai horad da wata babbar kungiya?'

    "Ina ganin idan namiji ne a gabansu suke tantancewa ba za su taba yi masa wannan tambayar ba."

    Amma kuma tana dariya ta kara da cewa: "Ba haka lamarin yake a Chelsea ba."

    Binciken wanda aka bayyana ranar Laraba ya nuna cewa wariyar da ake nuna wa mata a harkar wasan kwallon kafa na da yawa kuma ana yi sosai.

    Ya gano cewa kashi 63 da rabi na mata da ke aiki a bangaren wasan kwallon kafa na fuskantar shagube ko barkwanci na lalata, yayin da kashi 56 cikin dari suka ce ba a daukar wani mataki a kan yi musu hakan, bayan sun kai rahoto na wariyar a wurin aiki.

  3. Matashin ɗanwasa Ngumoha ya ƙulla kwantiragin farko da Liverpool

    Matashin ɗanwasan Liverpool Rio Ngumoha ya ƙulla yarjejeniyarsa ta farko ta sana'ar ƙwallon ƙafa da zakarun na Firimiya.

    A watan da ya gabata ne Ngumoha, mai shekara 17, ya ci wa Liverpool ƙwallon da ta ba ta nasara a kan Newcastle a cikin minti na 100 a wasansa na Firmiya na farko.

    Sai dai kuma Liverpool ba ta bayyana tsawon shekarun kwantiragin matashin ɗanwasan ba.

    Ɗanwasan na gaba gefen hagu, ya bar cibiyar renon matasan 'yanwasa ta Chelsea ne ya tafi Liverpool a watan Satumba na 2024, kuma tun daga lokacin ya buga wasa biyar na manya.

    A watan Janairu Ngumoha mai shekara 16 da kwana 135 ya zama ɗanwasa mafi ƙarancin shekaru da Liverpool ta taɓa sawa tun daga farkon wasa a karawar da ta doke Accrington 4-0 a gasar cin kofin FA.

    Haka kuma ya fara taka leda a gasar Zakarun Turai a karon farko a watan nan lokacin da Liverpool ta doke Atletico Madrid 3-0 a Anfield.

    Ngumoha ya taka wa Ingila wasa a matakai daban-daban na matasa inda ya yi wa tawagar 'yan ƙasa da shekara 19 ta ƙasar wasan farko a ranar 3 ga watan Satumba.

    Ana ɗaukarsa a matsayin tauraron ɗanwasa a tsakanin sa'o'insa a Chelsea amma kuma ya tafi Liverpool saboda yana ganin zai fi samun damar shiga tawagar mayna 'yan wasan a can.

    Ya kuma yi hakan ne duk da irin tabbacin da aka riƙa jaddada masa a Chelsea.

    Kociyan Liverpool Arne Slot ya sanya Ngumoha a hoton jerin 'yanwasansa na farko a wasan shirin tunkurar kaka a wannan shekarar, inda ya sa shi tun da farko a karawarsu da Athletic a watan Agusta.

    Minti biyu da fara wasa Ngumoha ya ɗaga raga.

  4. Iyaye da 'ya'yan da suka taka leda a tarihin gasar Premier

    A Firimiya akwai wani rukuni na daban da ya ƙunshi wasu tsofaffin 'yanwasan da suka taka leda a gasar ta Ingila kuma 'ya'yansu ma suka biyo sahu da wasan a wannan gasa.

    Wannan rukuni dai ya zama tamkar wani na musamman, domin ba kowa ne ɗanwasa ba ne da ya shiga tarihin gasar ta Firmiya, ɗansa ma kuma yake shiga wannan jerin.

    Waɗanda ke bakin gaɓar shiga wannan tarihi a yanzu su ne 'ya'yan tsohon ɗanwasan Ingila Emile Heskey, wanda ya yi ƙungiyoyi a Firimiya da suka haɗa da Leicester da Liverpool da Birmingham City da Wigan da Aston Villa.

    A ranar Laraba ne bayan da Manchester City ta ci Huddersfield 2-0 a wasaan cin kofin Carabao, sai kociyan City ya sanya Reigan da Jaden Heskey, 'ya'yan tsohon tauraron ɗanwasan na Ingila, Emile.

    Bayan shekara goma da mahaifinsu ya taka leda a wasansa na ƙarshe na wannan Kofi na EFL, sai kuma ga 'ya'yansa biyu a wasansu na farko a gasar kofin.

    A yanzu fatan waɗannan 'yanwasa biyu wa da ƙani -Jaden da Reigan shi ne su fara wasan Firimiya kuma da sun samu wannan dama za su kasance cikin wani rukuni na musamman, na 'ya'yan da mahaifansu suka yi wasa a Firmiya

    Ɗanwasan gaba na City Erling Haaland kusan shi ne fitacce a cikin jerin, kasancewar mahaifinsa, tsohon ɗan bayan Leeds da kuma City Alf-Inge.

    Justin Kluivert, ɗan tsohon ɗanwasan Newcastle da Netherlands Patrick, yana taka leda a Bournemouth, yayin da mai tsaron ragar Denmark Kasper Schmeichel ya yi koyi da mahaifinsa Peter wajen cin kofin Firimiya da Leicester City a 2016.

    Ɗanwasan gaba na Chelsea Liam Delap ɗa ne ga tsohon ɗan bayan Stoke City Rory, yayin da tsohon ɗan gaban Arsenal Ian Wright shi ne mahaifin 'yanwasan Manchester City biyu Shaun Wright-Phillips da Bradley Wright-Phillips.

  5. Ko yaushe Lammens zai fara tsare wa Man United raga?

    Cinikin Senne Lammens wanda ya kasance ƙila-wa-ƙala a ranar ƙarshe ta kasuwar saye da sayar da 'yanwasa ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda ke cike da dambarwa a wannan rana.

    Tun a farkon lokacin da aka buɗe kasuwar Manchester United ta nuna tana da sha'awa a kan mai tsaron ragar, kuma duk da cewa ƙungiyar ta ƙara tsananta sha'awar sayensa a makon ƙarshe na kasuwar, to amma duk da haka sai a ranar ƙarshe United ɗin ta motsa domin cinikin.

    Kuma a wannan lokacin, golan mai shekara 23 na ƙungiyar Royal Antwerp ta Belgium tuni yana kan hanyarsa ta zuwa Ingila, domin tabbatar da cewa yana kusa idan buƙatar hakan ta taso an cimma yarjejeniya.

    A ƙarshe dai ciniki ya faɗa - inda aka bayar da sanarwa da ƙarfe 10 da dare- sa'a goma bayan rufe kasuwar - kuma bayan mai tsaron ragar Aston Villa, wanda ya ɗauki Kofin Duniya da Argentina, ya haƙura da burinsa na zuwa Old Trafford, wanda shi ma kuma United ɗin ta sake nuna tana sonshi.

    Lammens ya bayyana zuwanshi United a kan fam miliyan 18.1 a matsayin burin da ya cika. Kuma ya yi fatan hakan zai zama farkon wani abu na musamman.

    To amma mako biyu bayan wannan ciniki, har yanzu muna jiran mu ga Lammens a wasa. Ba wanda ya sani ko kociyan Ruben Amorim zai sa shi a karon farko a wasan Firimiya a karawar gidan Brentford ranar Asabar.

    Ko ya sa shi a wasan da za su yi a gida da Sunderland ranar 4 ga watan Oktoba, ko kuma ya ci gaba da jiran tsammani.

  6. Amurka ta ce za ta yaƙi duk wani shiri na hana Isra'ila shiga gasar Kofin Duniya

    Amurka ta ce ba za ta amince ba kuma za ta tashi tsaye domin yaƙar duk wani yunƙuri na hana tawagar Isra'ila zuwa gasar ƙwallon ƙafa ta cin Kofin Duniya da za a yi a shekara mai zuwa - 2026, gasar da za a gudanar bisa haɗin gwiwa a Amurka da Kanada da kuma Mexico.

    Amurkar ta bayyana hakan ne sakamakon matakan da hukumomi da wasu ƙasashe ke shirin ɗauka da hana Isra'ila shiga harkokin wasu wasanni na duniya saboda aikata laifukan kisan kiyashi a yaƙin da take yi a Gaza.

    A wata sanarwa kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amurka ya gaya wa BBC cewa: ''Ba shakka za mu yi aiki tuƙuru mu dakatar da duk wani ƙoƙari na haramta wa tawagar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Isra'ila shiga gasar Kofin Duniya.''

    A farkon watan nan na Satumba wani kwamitin bincike na Majalisar Ɗinkin Duniya ya bayyana cewa Isra'ila ta aikata kisan-kiyashi a kan Falasɗinawa a Gaza.

    Wannan ne ya sa kwamitin wasu ƙwararru na Majalisar tare da Firaministan Sifaniya Pedro Sanchez suka yi kira da a sanya wa Isra'ila takunkumi a kan harkokin wasanni - Uefa da Fifa su hana ta shiga wasanninsu.

    A halin da ake ciki kuma a farkon mako mai zuwa ne hukumar ƙwallon ƙafa ta Turai - Uefa - wadda take shirya wasannin tace waɗanda za su je gasar Kofin Duniya a Turai, za ta iya yin wani taro domin tattauna yuwuwar dakatar da Isra'ila shiga wasannin, kamar yadda wasu rahotanni ke cewa.

    A kodayaushe Isra'ila na musanta cewa ta aikata kisan-kiyashi a Gaza, inda take cewa rahoton na Majalisar Ɗinkin Duniya ya jirkita al'amura.

  7. Saliba ya amince da sabon kwantiragi na shekara biyar da Arsenal

    Dan bayan Arsenal defender William Saliba ya amince da sabon kwantiragin shekara biyar da kungiyar.

    Shekara biyu ta rage a tawagar ḍanwasan na tawagar Faransa a yanzu kafin ya sabunta kwantiragin to amma kamar yadda aka sheda wa BBC a yanzu, zai tsawaita zamansa inda zai sa hannu a sabon kwantiragin a cikin kwanakin da ke tafe, domin ci gaba da zama a Emirates har zuwa shekara ta 2030.

    Saliba, mai shekara 24, ya koma Gunners daga kungiyar Saint-Etienne ta babbar gasar Faransa - Ligue 1 - a watan Yuli na 2019, amma kuma Arsdenal din ta mayar da shi kungiyar aro a kakar 2019-20.

    Arsenal ta kuma kara bayar da shi aro a kungiyarNice da kuma Marseille dukkaninsu na gasar ta Faransa.

    Tun bayan wasansa na farko a Arsenal a watan Agusta na 2022 ya zama daya daga cikin wadanda Arteta ya dogara da su a baya, kuma ya yi wa kungiyar ta arewacin Landan wasa 137.

    Kwazonsa ya sa har kungiyar Real Madrid ta nuna sha'awar sayensa.

    Da wannan sabon kwantiragi nasa da kuma tsawaita na Gabriel Magalhaes zuwa watan Yuni na 2029, Arteta ya kara karfafa bayan kungiyar Arsenal a burinsa kan gasar Firmiya da ta Zakarun Turai.

    A ranar Lahadi Arsela za ta je filin St James' Park don karawa da Newcastle a gasar Firmiya

  8. Leoni na Liverpool zai yi jinyar mako huɗu

    Mai tsaron bayan Liverpool, Giovanni Leoni zai yi jinyar mako hudu, bayan ranun da ya ji a wasansa na farko a kungiyar, inda Liverpool ta yi waje da Southampton daga Carabao Cup ranar Talata.

    Matashin mai shekara 18 ya koma Anfield a watan Agusta daga Parma - da wannan raunin na Leoni, saura yan wasa uku dake buga gurbin tsare baya daga tsakiya a tsaye da ya hada da Virgil van Dijk da Ibrahima Konate da kuma Joe Gomez.

    Tuni kuma kungiyar Anfield ta maye gurbin Leoni a Champions League da Federico Chiesa.

    Liverpool ta lashe dukkan wasa biyar da fara Premier League, wadda ke fatan sake cin kofin da ta lashe a kakar da ta wuce.

  9. An tsayar da ranar El Clasico tsakanin Real Madrid da Barcelona

    An tsayar da ranar da za a buga wasan La Liga tsakanin Real Madrid da Barcelona a wasan hamayya da ake kira El Clasico.

    Muhukuntan babbar gasar tamaula ta Sifaniya, sun ce za a yi karawar ce ranar 26 ga watan Oktoba a Santiago Bernabeu kuma mako na 1o kenan a gasar.

    Real Madrid ta lashe dukkan wasa shida da fara kakar nan, bayan doke Levante ranar Talata, kenan tana da maki 18, ita ce kan gaba a teburin La Liga.

    Ita kuwa Barcelona wadda take da maki 13 daga wasa biyar, za ta je gidan Real Oviedo ranar Alhamis domin buga fafatawar mako na shida.

    Wasannin Real Madrid kafin El Clasico:

    Spanish La Liga Ranar Asabar 27 ga watan Satumba

    • Atl Madrid da Real Madrid

    European Cup Ranar Talata 30 ga watan Satumba

    • Kairat Almaty da Real Madrid

    Spanish La Liga Ranar Asabar 4O ga watan Oktoba

    • Real Madrid da Villarreal

    Spanish La Liga Ranar Lahadi 19 ga watan Oktoba

    • Getafe da Real Madrid

    European Cup Ranar Laraba 22 ga watan Oktoba

    • Real Madrid da Juventus

    Spanish La Liga Ranar Lahadi 26 ga watan Oktoba

    • Real Madrid da Barcelona

    Wasannin Barcelona kafin El Clasico:

    Spanish La Liga Ranar Alhamis 25 ga watan Satumba

    • Real Oviedo da Barcelona

    Spanish La Liga Ranar Lahadi 28 ga watan Satumba

    • Barcelona da Sociedad

    European Cup Ranar Laraba 1 ga watan Satumba

    • Barcelona da Paris St-Germain

    Spanish La Liga Ranar Lahadi 5 ga watan Satumba

    • Sevilla da Barcelona

    Spanish La Liga Ranar Asabar 18 ga watan Oktoba

    • Barcelona da Girona

    European Cup Ranar Talata 21 ga watan Oktoba

    • Barcelona da Olympiakos

    Spanish La Liga Ranar Lahadi 26 ga watan Oktoba

    • Real Madrid da Barcelona
  10. Liverpool na shirin ba wa dan wasan tsakiyar Netherlands, Ryan Gravenberch, mai shekara 23 sabon kwantiragi na dogon zango.(talkSPORT, external)

    Arsenal na sha'awar sayen dan wasan gaban Japan Takefusa Kubo, mai shekara 24 daga Real Sociedad a lokacin kasuwar musayar 'yan wasa ta Janairu.(Fichajes - in Spanish), external

    An shaida wa Liverpool cewa ba za ta iya shawo kan Crystal Palace don ta sayar mata da dan wasan tsakiyar Ingila Adam Wharton, mai shekara 21, a kasuwar musayar 'yan wasa ta Janairu. (Teamtalk, external)

    Kungiyar Barcelona ta cimma matsaya da dan wasan tsakiya na kasar Netherlands Frenkie de Jong mai shekaru 28, wanda ya amince ya tsawaita zamansa har zuwa shekarar 2029 kan albashin da aka rage. (Mundo Deportivo - in Spanish), external

  11. Ko Isak ya shirya fuskantar Palace a Premier League?

    Alexander Isak ya fara ci wa Liverpool ƙwallo a Carabao Cup ranar Talata da ta fitar da Southampton da cin 2-1 a fafatawar zagaye na uku

    Wasa na uku kenan da ya buga wa ƙungiyar Anfield, bayan Champions League da Liverpool ta yi nasara 2-1 a kan Atletico Madrid ranar 17 ga watan Satumba.

    Ya buga wasan da Liverpool ta doke Everton 2-1 a gasar Premier League, wanda aka saka ci a minti na 67, amma bai ci ƙwallo ba.

    Hankali ya karkata a wasan da Liverpool za ta buga na gaba a Premier League da Crystal Palace.

    Shin ko Isak ya shirya karɓar gurbin mai cin ƙwallaye a Liverpool?

  12. Ƙungiyoyin da suka kai zagayen gaba a Carabao Cup

    • League Two: Grimsby Town
    • League One: Cardiff City da Wycombe Wanderers
    • Championship: Swansea City da Wrexham
    • Premier League: Brentford da Brighton da Crystal Palace da Chelsea da Fulham da Liverpool da kuma Wolverhampton.
  13. An fadawa Arsenal da Liverpool cewa babu tabbas game da makomar dan wasan Brazil Vinicius Junior mai shekara 25 a Real Madrid. (TBR Football, external)

    Kocin Fulham Marco Silva ya ce dan wasan tsakiya na Wales Harry Wilson, mai shekara 28, wanda Leeds ta so ta dauko lokacin bazara, zai tattauna kan tsawaita kwantiraginsa da su. (Sky Sports), external

    Leeds na neman dan wasa mai kai hari da kuma dan wasa tsakiya a kasuwar musayar 'yan wasa ta watan Janairu. (Football Insider), external

  14. Wasannin da za a buga zagaye na uku a Carabao Cup ranar Laraba

    • Huddersfield v Manchester City
    • Newcastle v Bradford
    • Tottenham v Doncaster
    • Port Vale v Arsenal (20:00)
  15. Mbappe ya ci ƙwallo bakwai da fara La Liga ta bana

    Real Madrid ta je ta doke Levante 4-1 a wasan mako na shida a La Liga da suka kara ranar Talata.

    Kylian Mbappe ne ya ci biyu daga ciki, kenan ya zura bakwai a raga da fara kakar nan.

    Da wannan sakamakon Real Madrid ce kaɗai ta lashe dukkan wasa shida da fara kakar nan ta kuma ci gaba da zama ta ɗaya a kan teburi da maki 18.

    Ranar Alhamis Barcelona wadda take da maki 13 za ta je gidan Real Oviedo a wasan mako na shida a babbar gasar tamaula ta Ingila.

  16. Madueke na Arsenal zai yi jinyar wata biyu

    Ana sa ran ɗanwasan Arsenal Noni Madueke zai shafe mako shida zuwa takwas yana jinya sanadiyyar Rauni da ya samu a gwiwa a wasan da ƙungiyarsa ta kara da Machester City ranar Lahadi.

    Sai dai an gano cewa raunin da ɗanwasan mai shekara 23 a duniya ya samu bai yi muni da yawa ba.

    Ɗanwasan wanda Arsenal ta ɗauko daga Chelsea gabanin fara kakar wasa da ake ciki, an sauya shi a wasan ne yayin da aka je hutun rabin lokaci, inda tun bayan wasan likitoci ke ƙoƙarin tantance girman raunin nasa.

    “Da alama Noni ba zai yi wasa ba na ƴan makonni, amma ba mu sani ba tukuna, sai mun sake yi wa ƙafar hoto a mako mai zuwa,” in ji mai horas da Arsenal Mikel Arteta a ranar Talata.

    A ranar Laraba Arsenal za ta kara da Port Vale a zagaye na uku na kofin Carabao.

    Wannan labari nakasu ne ga Arsenal da kuma tawagar Ingila, ganin yadda Madueke ya nuna hazaƙa daga farkon kakar nan.

    Idan abin da aka yi hasashe game da raunin ya tabbata, hakan na nufin Madueke ba zai koma filin wasa ba har sai cikin watan Nuwamba, wanda hakan zai sa ya gaza buga wasu muhimman wasanni ga Arsenal da kuma Ingila.

    Sai dai wasu na ganin abin zai zo wa Arsenal da sauki bayan dawowar ɗan wasanta Bukayo Saka daga jinya.

  17. Wasu wasannin da za a buga ranar Laraba

    UEFA Europa League wasannin farko a cikin rukuni

    • Braga da Feyenoord
    • Dinamo Zagreb da Fenerbahce
    • Freiburg da Basel
    • Malmo FF da Ludogorets
    • Midtjylland da Sturm Graz
    • Nice da Roma
    • PAOK da Maccabi Tel-Aviv
    • Real Betis da Nottingham Forest
    • Red Star Belgrade da Celtic

    Carabao Cup fafatawar zagaye na uku

    • Huddersfield da Mancester City
    • Newcastle United da Bradford
    • Port Vale da Arsenal
    • Tottenham da Doncaster
  18. Guardiola na fatan Haaland zai murmure kafin wasansu da Burnley

    Pep Guardiola na fatan Erling Haaland zai murmure kafin ranar Asabar da za su fuskanci Burnley a gasar Premier League.

    An sauya ɗan ƙwallon Norway a wasan da aka tashi 1-1 tsakanin Arsenal da Manchester City ranar Lahadi a Etihad, inda Guardiola ya ce ɗan wasan na fama da ciwon baya.

    City tana ta tara a teburin babbar gasar tamaula ta Ingila da tazarar maki takwas tsakani da Liverpool mai rike da kofin bara.

    City tana fama da ƴan wasan dake jinya da suka haɗa da Rayan Cherki da Rayan Ait-Nouri da Omar Marmoush, yayin da aka sauya Abdukodir Khusanov a wasa da Arsenal a karshen mako.

  19. Newcastle na fama da ƙamfar cin ƙwallaye a kakar nan

    Bayan da Newcastle United ta sayar da ɗan wasan da yake ci mata ƙwallaye, Alexander Isak ga Liverpool a bana, ta tsinci kanta a kamfar cin ƙwallaye a kakar nan.

    Isak ya zura 23 a raga a Premier League a kakar da ta wuce, shi ne ke biye da Mohamed Salah a yawan cin ƙwallaye a gasar.

    Ya ci wa Newcastle 38 a lik wato kaso takwas cikin ɗari, kuma yana da hannu a ci wa ƙungiyar ƙwallaye kaso 40 cikin 100.

    Sai dai a kakar nan Aston Villa ce mai karancin zura ƙwallaye a raga a bana, sai kuma Newcastle biye da ita.

    Ƙungiyar da Eddie Howe ke jan ragama ta zura ƙwallo uku a raga a wasa biyar a lik, guda biyu a wasa da Liverpool da ɗaya a karawa da Wolves.

    Ta kuma ci ɗaya a Champions League ranar 18 ga watan Satumba da Barcelona ta yi nasara 2-1 a St James Park.

  20. Shin ko ya dace da aka bai wa Dembele ƙyautar Ballon d'Or?

    Dan wasan Paris St-Germain, Ousmane Dembele ne gwarzon Ballon d'Or na 2025.

    Ƙyautar da ake bai wa dan wasan da yafi kowa fice a fannin taka leda a duniya a kakar da ta wuce – kuma a karon farko da ya lashe ƙyautar.

    Mai shekara 28-ya ci kwallo 35 da bayar da 14 aka zura a raga a wasa 53 a PSG a bara, wadda ta lashe kofi uku ciki har da Champions League.

    Ya yi kan-kan-kan a cin kwallaye a Ligue 1 mai 21 a raga, kuma shi ne fitatcen dan wasa a babbar gasar tamaula ta Faransa, kuma mafi kwazo a Champions League.

    Haka kuma PSG ta kai wasan karshe a Fifa Club World Cup a bara tare da Dembele, sai dai Chelsea ce ta lashe kofin a birnin a Amurka.

    Lamine Yamal ne na biyu sai Vitinha na uku da Salah na hudu da kuma Raphinya na biyar, Mbappe na bakwai yake.