Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Alhamis 07/05/2026

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Aisha Aliyu Jaafar da Nabeela Mukhtar Uba

  1. Ana ci gaba da jimamin mutuwar mutumin da ya kafa gidan talibiji na CNN

    Ana ci gaba da aikewa da saƙonnin ta'aziyya bayan mutuwar Ted Turner, mutumin da ya kafa kamfanin da ya mallaki gidan talabijin na CNN, wanda ya rasu yana da shekara tamanin da bakwai.

    Shugaban Amurka Donald Trump, ya bayyana attajirin a matsayin "ɗaya daga cikin jiga-jigan da suka sauya fuskar yaɗa labarai a duniya.

    Goggagiyar mai gabatar da shirye-shirye a CNN Christiane Amanpour na cikin waɗanda suka aike da saƙon ta'aziyyarsu.

    Ta ce ''ya sauya duniya, Ted shi ne ya kirkiri gidan talabijin na farko da ya shiga ko ina a faɗin duniya da ya ke watsa shirye-shirye babu kakkautawa''.

    Baya ga CNN saran tashohin da Ted Turner ya mallaka sun hada da TNT sports da Cartoon Network da kuma Turner Classic Movies

  2. Wasu iyalai masu alaƙa da ƙungiyar IS sun koma Australiya bayan shafe shekaru a Syria

    Wasu iyalai da suka ƙunshi mata huɗu da yara 9 da ke da alaka da ƙungiyar masu ikirarin jihadi na Islamic State, sun isa Australia a yau, bayan shafe shekaru a wani sansani a Syria.

    Ƴan sandan Australia sun yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar za a kama wasu daga cikin matan a kuma tuhume su.

    Komawarsu Australia dai ya fuskanci adawa mai ƙarfi a siyasance, amma masu fafutuka na ganin bai kamata a hukunta yaran saboda abin da iyayensu suka aikata ba.

    Yaran da ake tunanin shekarun su sun kama ne daga shekara shida zuwa sama - za su sami tallafi ta fannin kula da lafiyar kwakwalwarsu da kuma sauya musu tunani don kar su kasance masu tsattsauran ra'ayi.

  3. An tabbatar wa wani sojan Italiya ɗaurin shekaru 20 saboda sayar wa Rasha bayanai

    Wata kotu a Italiya ta tabbatar da hukuncin ɗaurin shekara 20 da aka yanke wa wani tsohon jami'in sojan ruwan Italiya bisa laifin sayar da wasu bayanan sirri ga Rasha, inda ta ƙi amincewa da ɗaukaka ƙarar da ya shigar.

    An kama Walter Biot, wanda kyaftin ne a rundunar sojin ruwa, a wani wurin ajiye motoci a birnin Roma shekara biyar da suka gabata, inda ya mika takardun sirri na kungiyar tsaro ta NATO ga jami'an ofishin jakadancin Rasha bayan an biya shi kusan dala dubu shida.

    Biot dai ya na zaman gidan yari na shekara 30 bayan wani hukunci na daban da wata kotun soji ta yanke masa akan laifuka makamantan waɗannan da ake tuhumnarsa da su.

  4. Yaƙin da ake yi a Iran na dab da zuwa ƙarshe - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya yi hasashen cewa yaƙin da ake yi a Iran na dab da kawo ƙarshe, inda ya ce mutane da dama sun fahimci dalilinsa na kawo ƙarshen burin Tehran na mallakar nukiliya.

    Shugaba Trump ɗin ya kuma shaida wa manema labarai cewa Iran ta 'amince' ba za ta mallaki makamin nukiliya ba, wani abu da har yanzu Iran ɗin ba ta tabbatar ba.

    Kalamansa na zuwa ne a yayin da Iran ta ce tana nazari kan daftarin da Amurka ta gabatar.

    A wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban Faransa Emmanuel Macron, Shugaba Iran Masoud Pezeshkian ya ce ba za a cimma wata yarjejeniya ba har sai an bayar da tabbacin kawo ƙarshen yaƙin da kuma kawo ƙarshen toshe tashohin jiragen ruwa Iran.

    Rahotanni a kafafen yaɗa labaran Iran sun kuma ruwaito cewa an sake buɗe filin jirgin sama na Tabriz.

  5. Isra'ila ta kashe ɗaya daga cikin manyan kwamandojin Hezbollah a harin da ta kai Beirut

    Wata majiya da ke kusa da kungiyar Hezbollah ta shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa an kashe ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ta a wani harin da Isra'ila ta kai a kudancin birnin Beirut na kasar Labanon a jiya Laraba.

    Wannan dai shi ne hari na farko da aka kai a yankin cikin kusan wata guda.

    Majiyar ta bayyana sunan kwamandan a matsayin Malek Ballout, wanda aka ce shi ne kwamandan ayyuka na rundunar Radwan ta ƙungiyar.

    Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce shi da kan sa ya bayar da umarnin kai harin da aka kai kan kwamandan rundunar mayakan na Hezbollah.

  6. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafin BBC Hausa kai-tsaye, muna muku maraba da zuwa shafinmu na yau Alhamis.

    A yau ma, za mu kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a duniya, kama daga yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran, da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za kuma ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta kamar Facebook da Instagram da YouTube da kuma X domin kallon bidiyo da kuma tafka muhawara.