Iran na takalarmu da yaki - Saudiyya

Bayanan bidiyo, Wani gidan talbijin na Yemen ya fitar da bidiyon yadda Saudiyyan ta kakkabo da makamin
Lokacin karatu: Minti 2

Yariman Saudiyya Mohammed Bin Salman ya zargi Iran da talakar yaki ta hanyar samar da makamai masu linzami ga 'yan tawayen Yemen.

Yariman ya danganta matakin a matsayin yaki, kamar yadda kafofin yada labaran Saudiya suka ambato shi yana shaidawa sakataren harakokin wajen Birtaniya Boris Johnson ta wayar tarho.

A ranar Asabar an kakkabo wasu makamai masu linzami kusa da Saudiyya.

A nata bangaren, Iran ta musanta zargin bai wa 'yan tawayen Houthi makamai wadanda ke fada da gwamnatin Yemen da ke samun goyon bayan dakarun kawance da Saudiya ke jagoranta.

Ministan harakokin wajen Iran Mohammad Javad Zarif ya danganta kalaman Yariman a matsayin ma su hatsari.

Wasu kafofin yada labarai da ke goyon bayan 'yan tawayen Houthi sun ruwaito cewa mayakan sun harba Burkan H2, wani nau'in makami mai linzami a filin saukar jirgi na Sarki Khaled da ke arewa maso gabashin Riyadh, wanda ke nisan kilomita 850 daga kan iyaka da Yemen.

Sai dai Saudiyya ta yi nasarar kakkabo makamin, yayin da wasu tarkacensa suka warwatsu a filin saukar jirgin.

Kungiyar kare hakkin bil'adama ta ce harba makamin mai linzami a tashar jirgin saman da fararen hula suke, ya kasance aikata laifukan yaki.

Saudi Crown Prince Mohammed bin Salman (24 October 2017)

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Yarima Mohammed ya ce yunkurin gwamnatin Iran na samar da manyan makamai ga 'yan tawayen Yemen tamkar mataki ne na kaddamar da yaki akan masarautar Saudiyya

Yarima Mohammed wanda ya yi Allah-wadai da harba makamin, ya ce yunkurin gwamnatin Iran na samar da manyan makamai ga 'yan tawayen Yemen tamkar mataki ne na kaddamar da yaki akan masarautar Saudiyya.

Minsitan harakokin wajen Iran Javad Zarif, ya yi tir da kalaman na Yarima a zantawar da ya yi da Mista Johnson ta wayar tarho bayan ministan harakokin wajen na Birtaniya ya tattauna da Yarima a ranar Talata.

Iran da Saudiyya sun dade suna yakin cacar-baka musamman kan karfin ikon mulki a Gabas Ta Tsakiya.

Kuma duk da cewa kasashen ba su taba yaki da juna ba amma a fakaice suna yakar juna ta hanyar goyon bayan bangarorin da ke rikici a wasu kasashe.

line
line
Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Houthi fighters shout slogans during the funeral procession of a senior member killed in fighting with Saudi-backed Yemeni forces, Sanaa, Yemen (6 November 2017)

Asalin hoton, EPA

Map showing Saudi Arabia, Riyadh and Yemen