'Fatanmu a zaɓen gwamnan jihar Edo'

Bayanan bidiyo, Latsa hoton sama ku kalli bidiyo:
'Fatanmu a zaɓen gwamnan jihar Edo'

A ranar Asabar 21 ga watan Satumba ne mazauna jihar Edo da ke kudu maso kudancin Najeriya za su kaɗa ƙuri'a a zaɓen gwamnan jihar.

Sama da mutum miliyan biyu ne ke da rajistar zaɓe a jihar mai ƙananan hukumomi 18 da rumfar zaɓe 4,519.

A wannan bidiyon, wasu 'yan asalin arewacin ƙasar mazauna jihar sun bayyana fatansu game da zaɓen.