Sarkin da ke koyar da yara a makaranta
Sarkin da ke koyar da yara a makaranta
A jihar Osun ta kudu maso yammacin Najeriya wani sarki na yin abin da ba a saba gani ba, inda yake koyarwa a wata makarantar yara marasa galihu.
Yayin da ake yi wa sarakuna kallon masu kare al'ada, yin ayyuka irin na sauran al'umma kamar koyarwa a makaranta, ana ganin tamkar bai dace da su ba.
Sai dai Sarki Adedokun Abolarin ya ce yana son sauya yadda ake tafiyar da mulki ta hanyar inganta rayuwar al'umma ta hanyar ba yara ilimi.



