Yaya ake ji idan gwamnatoci suka katse intanet?

Bayanan bidiyo, Yaya ake ji idan gwamnatoci suka katse intanet?
Yaya ake ji idan gwamnatoci suka katse intanet?

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

Intanet ta zama wani ɓangare na rayuwarmu ta yadda mutane da dama ba sa jin daɗin rayuwa idan babu shi a yau.

Amma a ƙasar iran, kwanan nan gwamnati ta katse sadarwar intanet wanda ya hana samun labarai da rahotannin abubuwan da ke faruwa a kasar sosai.

Hakan na zuwa ne sakamakon zanga-zangar da ta karade kasar, inda masu boren ke nuna fushinsu kan mutuwar wata matashiya Mahsa Amini da ta mutu lokacin da take tsare a hannun yan sanda.

Jami’an tsaro sun kama Mahsa ne da zargin cewa ba ta saka hijabi ba kamar yadda dokokin kasar suka tanadar.