Malamin da ke ci gaba da koyar da yara duk da ya yi ritaya

Bayanan bidiyo, Latsa hoton sama ku kalli bidiyo:
Malamin da ke ci gaba da koyar da yara duk da ya yi ritaya

Sani Adamu malamin firamare ne da ya yi ritaya a wannan shekarar, amma kuma ya ci gaba da zuwa koyar da yara a ƙwaryar birnin Kano da ke arewacin Najeriya.

"Gani na yi da na dinga zuwa wurin kalle-kalle, ko karta, ko hira gara na tara yara na dinga tuna musu karatun da aka yi musu," in ji malamin da ya shekara 35 yana koyarwa.

Salon koyarwarsa ya yi kama da irin wanda kowane yaro zai so saboda yadda yake haɗawa da nishaɗi da wasa da dariya.

Sani Adamu