Ba za mu raina Angola ba - Yusuf

Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
Ba za mu raina Angola ba - Yusuf

Ɗan wasan Super Eagles na Najeriya, Alhassan Yusuf ya bayyana cewa za su mayar da hankali sosai a karawar da za su yi da Angola duk da kallon da ake yi wa Angola na wadda ba ta shahara ba a harkar ƙwallon ƙafa.

Yusuf ya faɗi haka ne a tattaunawarsa da BBC yayin da tawagar Najeriyar ke yin atisaye a birnin Abidjan, gabanin karawarta da Angola a zagayen kwata-fainal.

Najeriya dai ta yi nasara ne a kan Kamaru da ci 2-0 yayin da Angola ta doke Namibiya da ci 3-0 a karawar zagayen ƴan 16.

A ranar Juma'a 2 ga watan Fabarairu ne Najeriya za ta kara da Angola a wasan na kwata-fainal a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta nahiyar Afirka, 2023 da ke gudana a Ivory Coast.