Ba za mu raina Angola ba - Yusuf
Ba za mu raina Angola ba - Yusuf
Ɗan wasan Super Eagles na Najeriya, Alhassan Yusuf ya bayyana cewa za su mayar da hankali sosai a karawar da za su yi da Angola duk da kallon da ake yi wa Angola na wadda ba ta shahara ba a harkar ƙwallon ƙafa.
Yusuf ya faɗi haka ne a tattaunawarsa da BBC yayin da tawagar Najeriyar ke yin atisaye a birnin Abidjan, gabanin karawarta da Angola a zagayen kwata-fainal.
Najeriya dai ta yi nasara ne a kan Kamaru da ci 2-0 yayin da Angola ta doke Namibiya da ci 3-0 a karawar zagayen ƴan 16.
A ranar Juma'a 2 ga watan Fabarairu ne Najeriya za ta kara da Angola a wasan na kwata-fainal a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta nahiyar Afirka, 2023 da ke gudana a Ivory Coast.



