Ku San Malamanku tare da Sheikh Aliyu Hammari Walama

Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon
Ku San Malamanku tare da Sheikh Aliyu Hammari Walama

An haife Sheikh Sheikh Aliyu Hammari Walama a garin Gombe da ke jihar Gombe a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Ya fara karatu a wajen kakansa wanda shi ne sarkin malaman Gombe, kafain daga baya a kai shi makarantar tsangaya ta Alaramma Yakubu Bara, in da ya sauke Qur'ani tare da karanta ƙananan littatafan fiqihu domin.

A ɓngeran karatun boko Shehin malamin ya yi karatun furamare da sakandire a Gombe inda ya zarce kwalejin kyo aikin shari'a da adinin musulunci inda ya samu shaidar karatu ta diploma.

Ya zarce jami'ar jihar Gombe inda ya samu digirinsa na farko a fannin ilimin tarihi, sannan ya tafi jami'ar Maiduguri inda ya sake samun wata digirin a fannin shari'a.

Ya samu horon aikin lauya a shekarar 2019 a makarantar horas da lauyoyi da ke Yola a jihar Adamawa.

Malamin ya koma Jami'ar Maiduguri inda yanzu haka yake digirinsa na biyu a fannin ilimin gado