Ku San Malamanku tare da Hamza Umar Assudani

Bayanan bidiyo, Danna hoton da ke sama domin kallon bidiyon:
Ku San Malamanku tare da Hamza Umar Assudani

Filin Ku San Malamanku na wannan mako ya tattauna da Malam Hamza Umar wanda aka fi sani da Assudani.

An haifi malamin a unguwar Kwarbai da ke cikin birnin Zariya a shekarar 1980.

Ya soma karatunsa na addini a gidansu, amma daga bisani an tura shi wurin wasu manyan malamai inda ya ci gaba da karatu.

Kazalika malamin ya shiga makarantar boko inda ya soma a makarantar firamare ta Lemu sanna ya je makarantar firamare ta Larabci, wato Provincial Arabic Primary School, wadda ya kammala a 1992.

Malam Hamza ya yi karatun sakandare a Jama'atu Arabic School da ke Zaria inda ya gama a 2000.

Daga nan ya tafi makarantar gaba da sakandare ta Munazzama da ke Kura a Jihar Kano.

Malamin ya kara da cewa daga bisani ne ya tafi kasar Sudan inda ya yi digiri kuma ya kammala a 2005.

Kazalika ya dawo Najeriya inda ya yi digiri na biyu wato Masters a Jami'ar Bayero da ke Kano a 2014.

Malamin ya ce akwai malamai da suka yi tarisi a rayuwarsa amma babu kamar Sheikh Ahmad Maqary Sa'id.