Yadda na sulale daga hannun ƴan fashin daji - Ɗalibi
Yadda na sulale daga hannun ƴan fashin daji - Ɗalibi
A ranar Alhamis 7 ga watan Maris ne ƴan fashin daji suka shiga wata makarantar gwamnati a garin Kuriga da ke ƙaramar hukumar Chikun a jihar Kaduna, suka sace ɗalibai zama da mata fiye da 280.
Lamarin ya faru ne a daidai lokacin da ɗaliban suka kammala taron safe, inda ƴan bindigar suka yi wa makarantar ƙawanya tare da kora ɗaliban zuwa cikin daji.
Wannan ɗalibin wanda ya kuɓuta ya shaida wa BBC cewa ya kwanta ne a cikin ciyawa, inda ya riƙa jan ciki kafin ya samu wurin buya.
A cikin wannan bidiyo ɗalibin ya bayyana irin wahalar da ya sha kafin samun kuɓuta da kuma halin da sauran ɗalibai suka kasance a ciki.
Sannan ya bayyana yadda ya samu komawa cikin gari bayan yin tafiya mai tsawo a cikin daji.



