Dattijon da ya auri mata 23 da haihuwar ƴaƴa 70

Ƴar'autarsa a halin yanzu tana da wata uku, babban ɗansa kuwa yanzu shekarunsa 53.
Yanzu shekarar Mista Isaac Adamo 78 a duniya. Yana zaune ne a garin Malabi na yankin Oromia a ƙasar Habasha, wato Ethiopia.
Ya auri matarsa ta farko lokacin yana da shekara 23. Amma a tsawon shekara 55 da suka gabata ya auri mata 23, kuma yana da ƴaƴa 70.
Ya ce bai fi shekara ɗaya ba yanzu da auren amaryarsa, wadda ita ce cikon matarsa ta 23.
"Na auri mata da yawa"
Isaac Adamo shahararren makiyayi ne, domin akwai lokacin da yake da dabbobi 800 a garkensa.
Ya ce ya auri mata da yawa ne saboda yana da dukiya.
"Nakan yi aure a duk lokacin da nake so saboda ina da shanu da yawa, inda da dukiya da kadarori," in ji shi.
"Babban abin da na dogara da shi a rayuwa shi ne kiwon dabbobi. Ina da raƙuma da shanu da awaki da yawa."
Duk da cewa jimillar matan da Isaac ya aura sun kai 23, amma ba a lokaci ɗaya ya zauna da su ba.
Yawancin matan da ya aura, ya auro su ne daga garuruwan Udat da Arero da Moyale, sai kuma wasu daga wasu garuruwan.
"Duk wadda na saki sai na maye gurbinta"
Isaac na yin amarya ne a duk lokacin da ya saki ɗaya daga cikin matansa.
"Idan na ga mace mai kyawu, sai na saki ɗaya daga cikin waɗanda nake tare da su, na auro wata," in ji shi.
Matarsa ta farko ta rasu, inda a yanzu yake zaune da mata uku.
"Yanzu ina da mata uku. Na rabu da 19," in ji shi.
Ya ce ya rabu da wasu matan ne bayan samun saɓani, wasu kuwa ya rabu da su ne haka kawai.
A cikin yaran nasa 70 da ya haifa, akwai maza 36 sai kuma mata 34.
Amma a yanzu Isaac ya ce ba ya da niyyar ƙara aure.
A cewar Isaac, idan aka haɗa ƴaƴansa da jikoki a yanzu sun kai 279.
Sai dai a yanzu dukiyarsa ta ja baya, ba kamar yadda take ba a baya.
Babban ɗansa sunan shi Ibrahim, yayin da ƙaramar ɗiyarsa kuma sunata Dahab.
Ya ce mutane da dama kan tambaye shi yadda yake tarbiyyar ƴaƴan nasa.











