Duk wanda zai ce a yi gaskiya 'yan Najeriya ba sa son ganin sa - ICPC

Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
Duk wanda zai ce a yi gaskiya 'yan Najeriya ba sa son ganin sa - ICPC

Matsalar cin hanci da rashawa ta gawurta kuma ta shiga jinin 'yan Najeriya ta yadda duk wanda zai ce a yi gaskiya, ko a kwatanta yin daidai, mutane na ɗaukar sa a matsayin wani bauɗaɗɗen wanda ba a maraba da shi.

Shugaban hukumar yaƙi da cin da hanci da rashawa ta ICPC Dr. Musa Adamu Aliyu ne ya bayyana haka a zantawar da muka yi da shi a kan batutuwa daban-daban da suka shafi hukumarsa.

Ya ce ICPC kuma tana mayar da hankali a kan yaƙi da lalata mata da 'yan mata a wuraren aiki da makarantu, matsalar da ya ce tana ƙaruwa har a ƙananan makarantun sakandire da na firamare.