Ban yi nadamar ɗage zaɓen Senegal ba - Macky Sall

Bayanan bidiyo, Ban yi nadamar ɗage zaɓen Senegal ba - Macky Sall
Ban yi nadamar ɗage zaɓen Senegal ba - Macky Sall

Shugaban ƙasar Senegal Macky Sall ya ce bai yi nadamar ɗage zaben ƙasar ba da ya kamata a gudanar a watan da ya gabata, lamarin da ya haifar da ƙazamar zanga-zanga a faɗin ƙasar.

A wata hira da shugaban ya yi da BBC, Sall ya fayyace cewa ya ɗauki matakin ɗage zaɓen ne saboda matsalolin zaɓen da 'yan majalisar suka nuna.

"Babu wani haƙurin da zan bayar, ban yi wani laifi ba, ina magana da kai a matsayin shugaban ƙasar Senegal. Dukkan matakin da aka ɗauka kan zaɓen sun kasance cikin tsarin doka da ka'idoji," in ji Shugaba Sall.