Ku San Malamanku tare da Sheikh Idris Muhammad Muhammad

Bayanan bidiyo, Ku latsa hoton sama don kallon bidiyo:
Ku San Malamanku tare da Sheikh Idris Muhammad Muhammad

Shirin Ku San Malamanku na wannan mako ya tattauna ne da Sheikh Idris Muhammad Muhammad, wanda aka haifa a birnin Lafiyar Barebari a shekarar 1974.

Ya fara karatunsa na firamare a Lafiya, kafin ya tafi zuwa birnin Jos inda ya yi sakandire.

Ya samu damar shiga Jami’ar Al-Azhar a ƙasar Masar lokacin da yake gab da kammala karatun difloma a Jos.

Sheikh Idris Muhammad ya kammala karatun digirinsa na biyu a Jami’ar Jihar Nasarawa, kafin daga bisani ya koma aiki a Jami’ar Tarayya ta Lafiya.

Malamin ya ce a yanzu haka shi ne shugaban tsangayar nazarin Larabci a Jami’ar Tarayya ta Lafiya.