Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Yadda satar ɗalibai ke barazana ga makomar ilimi a arewacin Najeriya
Satar ɗalibai na neman zama ruwan dare musamman a arewacin Najeriya.
Daga watan Disamba, Ɗalibai da dama ne aka sace daga makarantu a arewa maso yammacin Najeriya, wanda ke nuna wani mummunan yanayi mai matukar tayar da hankali a matsalar satar mutane domin neman kuɗin fansa.
Ana kuma ganin matsalar satar ɗaliban babbar barazana ce ga ilimi a yankin arewacin Najeriya. Me ya sa ƴan bindiga ke kai hari makarantu da satar ɗalibai? BBC ta duba wannan batu.