Covid-19: Gargadi ga masu kin sanya takunkumi a Najeriya

Bayanan bidiyo, Gargadi kan masu kin sanya takunkumi a Najeriya

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

Hukumomi a Najeriya sun wajabta sanya takunkumi a bainar jama'a sakamakon ci gaba da yaduwar cutar korona.

Shugaban kasar Muhammadu Buhari ya amince a ci tarar duk mutumin da aka samu da laifin kin sanya takunkumin.

Tuni hukumomi a Abuja babban birnin kasar suka soma cin tarar masu karya wannan dokar.

Cutar korona na ci gaba da yaduwa a kasar, lamarin da ya sa hukumomi suke gargadin mutane kan hadarin kamuwa da ita.

Wannan bidiyon ya yi bayani kan wannan batu.

Wasu bidiyon da za ku so ku kalla