Fursunoni 200 sun tsere daga gidan yari

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Umaymah Sani Abdulmumin and Nasidi Adamu Yahaya

  1. Rufewa

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni, sai kuma gobe Alhamis idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Za ku iya ziyartar shafinmu na Facebook ko Twitter ko kuma Instagram domin duba wasu labaran da muka wallafa ko kuma tafka muhawara a kansu.

  2. MDD na zargin Venezuela da take haƙƙin bil adama

    Masu bincike na Majalisar Ɗinkin Duniya na zargin gwamnatin Venezuela da aikata laifuka da suka saɓa wa rayuwar bil adama.

    Masu binciken sun bayyana cewa gwamnatin ta Venezuela ta aikata laifukan ne a yunƙurinta na daƙile 'yan adawa a ƙasar.

    Wani rahoto da aka samu ya nuna yadda gwamnatin ta kashe mutane ba bisa ƙa'ida ba, da ɓatar da mutane da kuma azabtarwa.

    Masu binciken sun lissafo sama da manyan jami'an tsaro 40 da ake zarginsu da hannu a aikata laifukan.

    Rahoton ya kuma bayyana cewa Shugaban ƙasar Nicolas Maduro da kuma ministansa na cikin gida na sane da laifukan da aka aikatawa, kuma a wani zubin ma, su ne ke bayar da umarnin yin hakan.

    Sai dai gwamnatin ta Venezuela ta ce wannan rahoton duk na ƙarya ne.

    Za a miƙa rahoton ga Hukumar Majalisar Ɗinkin Duniya da ke kula da haƙƙin bil adama a mako mai zuwa, inda a nan ne Venezuela za ta samu damar mayar da martani kan zarge-zargen da ake yi mata.

  3. Ba ni da matsala da Dele Alli - Mourinho

    ...

    Asalin hoton, TOTTENHAM HOTSPUR FC

    Kocin Tottenham Jose Mourinho ya ce ba shi da wata matsala da Dele Alli a yayin da suke shirin fafatawa da Lokomotiv Plovdiv a wasan neman gurbin shiga gasar Europa.

    An maye gurbin Alli lokacin da aka tafi hutun rabin lokaci a wasan da Everton ta doke su da ci 1-0 ranar Lahadi.

    Mourinho ya ce yanayin wasan da ake yi guda daya neman cancantar shiga gasar Europa na wannan karon daban yake saboda cuar korona - kuma hakan ya sa bai za su iya kasa a gwiwa ba.

    Ga cikakken labarin a nan:

  4. An yanke wa wani mayaƙin al-Shabab ɗaurin rai da rai a Kenya

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Wata kotun sojoji a Somalia, ta yanke wa wani mai iƙirarin jihadi hukuncin ɗaurin rai da rai sakamakon samunsa da laifi a wani hari da aka kai a wani sansanin sojin Amurka da ke a Kenya.

    An kuma samu Farhan Mohamud Hassan da laifin zama ɗan ƙungiyar al-Shabab, wadda ƙungiya ce da ke da alaka da al-Qaeda kuma take da hedikwatarta a Somalia.

    Harin da suka kai shi ne na farko kan sojojin Amurka a Kenya, sojojin na da mayaƙa 20,000 da ke yaƙar masu iƙirarin jihadi a Somalia.

    Amurkar na yawan kai hare-hare kan ƙungiyar al-Shabab a Somalia.

  5. An sassauta dokar kullen Afrika Ta Kudu mai tsananin tsauri

    ..

    Shugaban Afrika Ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya bayyana sake sassauta dokar kulle a ƙasar.

    Dokar kullen Afrika Ta Kudu na ɗaya daga cikin mafi tsauri da ƙasashen duniya suka sa a lokacin kullen annobar korona.

    Mista Ramaphosa ya bayyana cewa ƙasar ta tsallake lokaci mai tsanani da ta fuskanta na annobar, wanda hakan ya sa ƙasar za ta buɗe iyakokinta ga baƙi masu son shiga ƙasar. Sai dai kafin su shiga ƙasar, sai sun bayar da sakamakon gwajin da ke nuna cewa ba su ɗauke da cutar ta korona.

    Za a rage lokacin dokar fitar dare, za a ci gaba da sayar da barasa, amma dokar saka takunkumi da kuma bayar da tazara a tsakani na nan daram-dam.

  6. Fursunoni 200 sun tsere daga gidan yarin garin Moroto

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Sama da fursunoni 200 ne suka tsere daga wani gidan yari a garin Moroto da ke arewa maso yammacin Uganda.

    An bayyana cewa fursunonin sun gudu da bindigogi 15 da harsasai masu yawa.

    Fursunonin sun harbe wani soja wanda ya yi yunƙurin tare su. Tuni dai jami'an gidan yari da kuma sojojin ƙasar suka ƙaddamar da wani shiri na musamman domin gano su.

    Mai magana da yawun sojin ƙasar Birgediya Janar Flavia Byekwaso, ya bayyana cewa har yanzu sojojin suna bata kashi da fursunonin.

    An kama fursunoni biyu an kuma kashe ɗaya.

  7. MINTI ƊAYA DA BBC - LABARAN YAMMA 16/09/2020

    Bayanan sautiLatsa alamar lasifikar da ke sama domin sauraren labaran
  8. 'Duka ƙasashen Afrika sun nemi FIFA ta ba su tallafin kuɗi lokacin korona'

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Duka ƙasashen Afrika sai da suka nemi Hukumar Kwallon Ƙafa Ta Duniya wato FIFA ta ba su tallafin korona.

    "Ƙasashe 54 na nahiyar sai da suka nemi a ba su kuɗi," in ji mai magana da yawun hukumar a wata hirarsa da sashen wasanni na BBC.

    Ƙungiyar ta FIFA ta ce za ta bai wa ƙasashe 211 dala biliyan 1.5 da kuma hukumomin ƙwallon ƙafa na nahiyoyi shida.

    A ranar Laraba, FIFA ta bayyana cewa annobar korona ta lashe tattalin arziƙin ƙwallon ƙafa na kusan dala biliyan 14.

  9. Hukumomi a Sudan sun kama mutum 41 bayan kama sunduƙai cike da ammonium nitrate

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a Sudan sun kama mutum 41 bayan sun samu nasarar ƙwace abubuwan fashewa masu ɗimbin yawa.

    Abubuwan sun haɗa da sunduƙai huɗu ɗauke da sinadarin ammonium, wanda shi ne sinadarin da ya fashe a Beirut ya kuma yi sanadiyar mutuwar mutane da dama a watan da ya gabata.

    Mai shigar da ƙara a ƙasar ya bayyana cewa yawan sinadarin da aka kama ya isa ya ƙone birnin Khartoum.

    Mai magana da yawun jami'an tsaron ƙasar ya bayyana cewa ana ta fargabar cewa akwai wasu ɓata gari da ke ƙoƙarin yin ƙafar ungulu ga gwamnatin riƙo ta Sudan, amma dai bai gabatar da wata shaida ba.

  10. Attajirin Najeriya Femi Otedola ya burge 'ya'yansa da motocin Ferrari Portofino

    ...

    Asalin hoton, DJ CUPPY

    Attajirin nan na Najeriya wanda ya shahara a kasuwancin man fetur Femi Otedola ya burge 'ya'yansa mata uku inda ya saya musu motocin kece raini kirar Ferrari Portofino.

    Florence Ifeoluwa Otedola wadda aka fi sani da DJ Cuppy ta wallafa hotunan motocin da mahaifinsu ya saya musu a shafukanta na sada zumunta ranar Laraba.

  11. Aston Villa ta sayi golan Arsenal Martinez a kan £17m

    Martinez

    Asalin hoton, Getty Images

    Aston Villa ta sayi gola Emiliano Martinez daga Arsenal a kan £17m.

    Dan wasan na Argentina mai shekara 28, wanda ya fito a wasa sau 23 a kakar wasan da ta wuce, kuma ya buga karawar da suka doke Chelsea a gasar cin kofin FA, ya tsawaita zamansa zuwa shekara hudu.

    Kocin Villa Dean Smith ya ce Martinez zai zama "daya daga cikin manyan 'yan wasa a wannan kungiyar a nan gaba".

    Martinez ya bar Arsenal shekara 10 bayan ya je kungiyar a tawagar matasa a 2010.

  12. Isra’ila ta kai hare-haren sama na ramuwa zuwa Gaza

    israila

    Asalin hoton, Getty Images

    Isra’ila ta kai wasu hare-haren sama zuwa Gaza, kan abin da ta kira ramuwa kan harin da mayakan Faladinawa suka kai mata.

    An kai harin ne jim kadan bayan bikin da Amurka ta karbi bakunci na sanya hannu kan yarjejeniyar diflomasiyya tsakanin kasashen Baharin da Hadaddiyar Daular Larabawa da kuma Isra’ila.

    Falasdinawa sun kira wannan yarjejeniya a matsayin butulci – suna cewa kamata ya yi a ce an yi wannan yarjejeniya ne kawai idan Isra’ila ta daina mamayar inda suke.

    Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin wani kokari ne na mayar da hannun agogo baya.

    Natanyahu ya ce ban yi mamaki ba da wannan harin da Falasdinawa suka kai, dai-dai lokacin da ake kafa wani tarihi.

    Suna son dawo da hannun agogo baya ne, kuma ba za su yi nasara ba.

  13. Ƴan sanda sun kama sojoji kusa 100 kan zarginsu da alaka da mai wa’azin Musulinci a Turkiyya

    Erdogan

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni na cewa ‘yan sanda a Turkiyya sun kama sama da mutum 100 – mafi yawansu sojoji, kan zarginsu da alaka da mai wa’azin Musulincin nan da Turkiyya ta zarga da yunkurin juyin mulki a 2016.

    Kamfanin dillancin labarai na kasar ya ce masu gabatar da kara a Santambul ne suka ba da izinin kama mutum 132, tare da kai samame kan wasu gwammai a wasu yankuna da dama.

    ‘Yan sanda masu yaki da ta’addanci sun ce suna ci gaba da binciken sauran mutanen da ake zargi.

    Wannan ne samamen baya-bayan nan da aka kai kan magoya bayan malamin nan da ke zaune a Amurka, Fethullah Gulen, wanda ya musanta hannu cikin yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba.

  14. 'Bidiyon boge ake yaɗa wa kan kisan wata mata a tuɓe'

    Ministan harkokin tsaron Mozambique ya ce bidiyon sojojin nan da ke nuna sun kashe wata mata a tuɓe da ake zargin ƴar ta’adda ce ba na gaskiya ba ne.

    Jaime Neto ya yi ikirarin an gyara hoton bidiyon ne domin dakushe kokarin dakarunsu da ke fafutikar ganin bayan masu ikirarin jihadi a Arewacin ƙasar.

    Ya ce za a kama wadanda suka yi wannan aikin kuma a hukunta su.

    Gwamnatin Mozambique ta sha musanta cewa sojojinta na cin zarafin mutane a yakin da suke da masu ikirarin jihadi, duk da sahihan rahotannin duka da azabtarwar da aka ga suna yi.

    A ranar Litinin ne aka wallafa wani hoton bidiyo a kafafen sada zumunta da ya nuna wasu sojojin ƙasar suna dukan wata mata kafin daga bisani su harbeta.

  15. Wani mutum ya kutsa majalisa dauke da kan yaro a hannun sa

    Uganda

    Asalin hoton, Getty Images

    'Yan sanda a Uganda sun ce kan wani yaro da aka kama wani mutum dauke da shi ya na ƙoƙarin kutsa wa cikin majalisa - na wani gangan jiki ne da aka tsinto a Masaka, kudu maso yammacin birnin Kampala.

    Mutumin da ke ɗauke da shurin kaya, Joseph Nuwashaba mai shekara 22 yana hannun ƴan sanda da ke bincike mai zurfi.

    Wasu iyalai a Masaka sun kai korafin batar ɗan su kuma yanzu haka ƴan sanda na son a yi binciken kwayoyin halitta domin tabbatar ko kan ɗan su ne.

    Iyalan sun ce sun dau Mr Nuwashaba aiki don taimaka musu a gona. Yanzu haka an shirya yi masa gwajin ƙwaƙwalwa.

    Mr Nuwashaba ya shaida wa ƴan sanda bayan cafke shi cewa zai kai wa kakakin majalisa Rebecca Kadaga ne sakon kan.

    Rebecca dai ba ta ce uffan akan batun ba. Sai dai ta shaida wa majalisa a ranar Talata cewa ta na jiran sakamakon binciken yan sanda.

  16. Buhari ya fitar da tambarin cika shekara 60 na ƴancin Najeriya

    Najeriya

    Asalin hoton, PRESIDENCY

    Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya kaddamar da tambarin bikin cikar Najeriya shekara 60 da samun ƴancin kai. Tambarin kalar tutar kasar na dauke da sakon haɗin-kan kasa.

    Najeriya

    Asalin hoton, PRESIDENCY

    Shugaba Buhari ya kaddamar da wannan tambari ne a taron majalisar ministoci da ya jagoranta a yau Laraba a Abuja.

  17. A saurari labaran duniya cikin Minti daya da BBC na Rana

  18. Majalisar Dinkin Duniya ta yi fushi kan ɗaure wanda ya ɓatanci ga Musulunci a Kano

    kANO

    Asalin hoton, AFP

    Hukumar kula da ilimin kananan yara ta Unicef ta nuna "damuwarta matuƙa" kan hukuncin da aka yanke wa wani yaro ɗan shekara 13 kan laifin ɓatanci ga addini.

    A watan Agusta, wata kotun shari'ar musulunci a jihar Kano ta yankewa Omar Farouq hukuncin ɗaurin shekara 10.

    Hukuncin "ba daidai ba ne .. ya saɓa ka'idoji da sharudan kare haƙƙin yara da Najeriya da ita kanta jihar Kano ta sanyawa hannu," a cewar Pater Hawkins jami'in Unicef a Najeriya

    Hukunci ya saɓa da yarjewar Majalisar Dinkin Duniya kan haƙƙin yara na 1991, da Najeriya ta aminta da shi, a cewar sanarwar Unicef.

    Unicef ta buƙaci gwamnatin Tarayya da ta jaha su gaggauta nazarin shari'ar domin sake hukunci.

    Tun koma wa kan mulkin dimokuradiya a 1999 jihohi da dama suka rungumi tsarin shari'ar musulunci a arewacin Najeriya.

  19. Kim Kardashian ta bi sahun fitattun mutane wajen ƙauracewa Facebook da Instagram

    Kim Kardashian

    Asalin hoton, Reuters

    Kim Kardashian West da fitattun mutane da dama sun sanar da cewa za su ƙauracewa shafukan su na sada zumunta domin zanga-zanga kan kalaman "ɓatanci da farfaganda da boge" da ake yaɗa wa.

    "Labaran bogen da ake yaɗa wa a sociyal midiya na da tasiri sosai," a cewar Kardashian a wani sako da ta wallafa ranar Talata.

    Wannan wani mataki ne na nuna goyon-baya ga gangamin #StopHateforProfit da ƙungiyoyin fara hula masu fafutika suka shirya.

    Fitattun mutanen da suka hada da Leonardo DiCaprio da Sacha Baron Cohen da Jennifer Lawrence, da mawaƙiya Katy Perry za su ƙauracewa shafukan su na sada zumunta na tsawon sa'a 24 a ranar Laraba.

    Katy Perry da Orlando Bloom

    Asalin hoton, Getty Images

    Shi ma mai fito wa a fina-finai Ashaton Kutcher, da ke da milyoyin mabiya ya bi sahu, sannan ya ce bai kamata ake amfani da wannan "kafa wajen yaɗa labaran ƙiyayya da ingiza rikici".

    An dai jima ana tafka muhawara kan hanyoyin kawo ƙarshen labaran boge da ƙiyayya da ke yaɗa wa a shafukan sada zumunta.

  20. Kamaru ta gargadi masu shirin aiwatar da zanga-zanga

    Gwamnatin Kamaru ta sake aike gargaɗi ga magoya bayan jam’iyyar MRC da Maurice Kamto ke jagoranta game da yunkurin da take yi na shirya abinda ta kira zanga-zangar lumana a ranar 22 ga wannan watan.

    Ministan harkokin cikin gida ya bayyana daurin rai-da-rai a matsayin hukunci kan duk wani wanda aka kama a kan titi yana zanga-zanga.

    Ministan ya bayyana zanga-zangar a matsayin haramtacciya, don haka yake cewa ba za su lamunce wa hakan ba.

    Gwamnatin dai ta sake jadada cewa fitowar jama'a da sunan zanga-zanga kokari ne na kifar da gwamnatin da aka zaba ta hanyar dimokuradiya.