Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da suka faru ranar Juma'a

Shafin da ke kawo labaran abubwan da ke faruwa kai tsaye a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da Chadi da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Sagiru Kano Saleh and Halima Umar Saleh

  1. Rufewa

    Jama'a a nan muka kawo karshen labarun kai tsaye na yau daga nan sashen Hausa na BBC - BBCHAUSA.COM.

    Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu. Sagir Kano Saleh da Halima Umar Saleh ke maku fatan alheri, mu kwana lafiya.

    Ku duba kasa domin ganin abubuwan da suka faru a yau Juma'a.

    Idan Allah Ya kai mu za mu ci gaba da kawo maku karin wasu labaran.

  2. Alhassan Doguwa ya jawo ce-ce-kuce a Twitter, Zuwa da matansa majalisa ya kawo mahawara

    'Yan Najeriya na tofa albarkacin bakunansu kan yadda dan majalisar wakilan kasar Alhassan Ado ya gabatar da matansa a zaman majalisar na jiya Laraba.

    Bidiyon ya nuna Doguwa wanda shi ne shugaban masu rinjayen majalisar yana tinkaho a gaban majalisar cewa shi ''tsayayye ne a majalisar da ma a gidansa.''

    Dan majalisar ya dawo zauren ne bayan samun nasara a zaben ranar Asabar da ta gabata. A baya kotun sauraren kararrakin zabe ta soke nasararsa a zaben watan Maris na shekarar 2019.

    Da yake jawabi dan majalisar ya bukaci matan nasa su mike.

    ''Mai girma shugaban majalisa ina sanar da cewa a yau ina tare da matana guda hudu masu alfarma. Halima na iya mikewa, Umma ma haka,'' inji shi yayin da takwarorinsa ke ta sowa.

    Ya kara da cewa ''Mai girma shugaban majalisa matan nan nawa su hudu sun haifa mani 'ya'ya 27, kuma ina fatan samun kari.''

    “Wani dalili kuma shi ne domin in sanar da kai cewa kamar yadda 'yan majalisa ke ce mani mai fada a ji, karfin fada a ji ba ba a majalisa ba ne kadai .... har a gida... domin ina kula ne da mace hudu,'' inji Doguwa.

    Kalaman nasa sun jawo mahawa a tsakanin masu goyon bayan hakan wasu kuma na kushewa.

  3. KAROTA ta kama jabun magunguna, A shago daya an kwace kwali 28 na kwayoyi

    Hukumommi a jihar Kano sun kama kwalayen jabun magunguna a jihar Kanon Najeriya.

    Jami'an gwamnatin jihar sun kwace kwalaye 28 na kwayoyin kara karfin 'saduwa' ne a wani kanti a da ke kwaryar birnin.

    Wani jami'in hukumar ya sufurin jiihar KAROTA ya shaida wa BBC cewa sun kai samame a kantin sayar da jabun magungunan ne tare tare da tsare mai shagon bayan samun bayanan sirri.

    Tuni hukumar KAROTA ta mika kwayoyin ga ma'aikatar lafiya ta kasar domin ci gaba da bincike.

    Sai dai bai yi bayanin yadda KAROTA ta gano cewa magungunan na jabu ne ba.

  4. Yadda annobar Coronavirus za ta shafi cinikayya a Afirka

    Dakatar da zirga-ziga zuwa China da kamfanonin jiragen saman Afirka ke yi saboda barkewar cutar coronavirus, na haifar da damuwa cewa hakan zai jefa kasuwancin kasashen nahiyar a mawuyacin hali.

    Dangantaka ta kudade tsakanin Sin da Afirka ta fara nisa sosai a 'yan shekarun nan, kamar yadda yawan masu yawon shakatawa na kasar Sin ke samu.

    Duk da yake yawancin cinikayyar ta kunshi jigilar mai da albarkatun kasa zuwa China, kasashe da dama da suka hadar da Rwanda, Kenya da Afirka ta Kudu suna fitar da albarkatun noma ta sama ne.

    Kamfanin sufurin jiragen sama na Kenya Airways da kamfanin jiragen sama mallakar kasar Rwanda sun dakatar da zirga-zirgar jiragen su har sai baba ta gani. Kamfanin jiragen saman Habasha ya ce zai ci gaba da zirga-zirga sama a yanzu. Kawo yanzu ba a tabbatar da bullar cutar a Afirka ba.

  5. Neman a binciki barkewar rikici a Sudan

    Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun bukaci a gudanar da bincike kan barkewar rikicin kabilanci a yankin Darfur na kasar Sudan.

    Rikicin ya yi sanadiyyar mutuwar mutum fiye da saba'in bayan wasu dubu hamsin da ke gudun yi hijira.

    Kungiyoyin Kare Hakkin Bil-Adama na kasa da kasa sun ce makiyaya larabawa sun kai harin ramuwar gayya kan sansanin Krinding kusa da garin Geneina a cikin kwanakin ukun karshen watan Disamba.

    Daga cikin wadanda suka kai harin akwai mutum sama da hamsin dake sanye da kakin dakarun rundunar Rapid Support Forces, da ke adawa da gwamnatin kasar.

    Wakilin BBC ya ce a baya an yi ta zargin dakarun rundunar da cin zarafin fararen hula a Sudan.

  6. Hotuna: Shugaba Buhari a lokacin da yake gana wa da sabon gwamnan Imo, Da kuma shugaban jam'iyyar APC a fadarsa a Abuja yau Juma'a

    President @MBuhari receives new Governor of Imo State, His Excellency, Hope Uzodinma and APC National Chairman Comrade Adams Oshiomole today, in his office, at the State House, Abuja.

  7. Za a yi bincike kan rikicin kabilanci a Sudan

    Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun yi kira da a gudanar da bincike kan barkewar rikicin kabilanci a yankin Darfur na kasar Sudan, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 70 kuma kusan50,000 ne suka yi hijira.

    Kungiyoyin Kare Hakkin Bil-Adama na kasa da kasa da kungiyoyin kare hakkin dan adam sun ce makiyayan Larabawa sun kai hari kan sansanin Krinding kusa da garin Geneina a cikin kwanakin ukun karshen watan Disamba.

    Hare-haren sun kasance kamar daukar fansa game da kisan 'yan uwansu.

    Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun ce daga cikin wadanda suka kai harin wanda sama da mutum 50 na sanye da kakin rundunar Rapid Support Forces, dakaru ne da ke adawa da gwamnatin kasar.

    Wakilin BBC ya ce akwai rade-radin da aka yi ta yadawa a baya kan yadda dakarun suka rika cin zarafin fararen hula a Sudan.

  8. 'Yan acaba na zanga-zanga kan hana su aiki a Legas

    Masu haya da babura na zanga-zanga saboda haramta sana'arsu da gwamantin jihar Legas ta yi.

    Gobe Asabar 1 ga watan Fabrairu ne dokar hana acaba a jihar za ta fara aiki.

    Masu haya da babura na kamfanonin sufuri na Opay da GOKADA da Maxkeke ne suka jagoranci zangar kin amincewa da haramcin a wasu kananan hukumomin jihar.

    Haramcin ya hada da masu tuka babura masu kafa uku da ake kire Keke Napep a jihar.

    Gwamnatin jihar ta ce ta haramta aikin masu baburan ne saboda karya doka da hadurran da masu sana'ar ke haddasawa.

    Za a aiwatar da dokar haracin ne a kan dukkan manyan tituna da gadoji a jihar.

    Sanarwar gwamnatin ta ce matakin zai ba wa matasa damar samun wasu sana'o'in hannu masu tsafta domin sana'ar acaba ba mai dorewa ba ce.

  9. An mari dan Majalisa a zauren majalisa Uganda, An kwanatar da shi a asibiti bayan takwaransa ya mare shi

    Wani dan majalisar dokoki ya mari takwaransa har aka kwantar da shi asibiti a majalisar dokokin Uganda.

    Fada ta kaure tsakanin 'yan majalisar da suka damabce a harabar majalisar ne bayan dayansu ya zargi takwaransa da neman jama'ar mazabarsa kada su zabe shi.

    Jaridar Daily Monitor ta kasar ta ruwaito dan majalisa Anthony Akol mai wakiltan Kikak ta Arewa na cewa ya mari Odonga Otto na mazabar Aruu domin kare kansa.

    Otto na kwance a asibiti a birnin Kampala bayan lamarin da ya auku tsakanin 'yan majalisar daga jam'iyya radawa ta Forum for Democratic Change.

    Akol ya yi ta bin Otto a harabar majalisar inda yake tambayarsa dalilinsu na ce wa mutane kar su zabe shi.

    Mista Otto ya shaida masa cewa dalilinsa na yin hakan shi ne saboda Akol din ya sayar da wani fili mallakin al'umma.

    Jin hakan ke da wuya sai Akol ya tsinke Otto da mari kafin fada ta kaure taskaninsu kafin wani dan majalisar ya zo ya raba su.

    Dan majalisar ya ce ya aikata hakan ne domin kare kansa.

  10. Matsalar tsaro: 'Yan majalisar PDP sun yi zanga-zanga, Sun je ofishin jakadancin Amurka da Birtaniya

    'Yan majalisa daga jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya sun gudanar da zanga-zangar lumana kan matasalar tsaro a kasar.

    'Yan majalisar tare da shugaban jam'iyyar Uche Secondus sun yi tattaki zuwa ofishin jakadancin Birtaniya inda suka mika takardar kokensu.

    Hakan na zuwa ne kwana biyu bayan shugaban marasa rinjaye a majalisar dattawa kasar, Sanata Eyinnaya Abaribe, ya bukaci shugaban kasar Muhammadu Buhari ya yi murabus saboda kasa magance matsalar tsaron kasar.

    Bayan nan sun kuma je ofishin jakadancin Amurka inda nan ma suka mika takarda.

    A ranar Litinin shugabannin jam'iyyar za su ci gaba da wannan tattaki da mika takardun koke a ofishin Majalisar Dinkin Duniya da na Tarayyar Turai a Abuja.

  11. Kansar mahaifa za ta bace a doron kasa nan da shekara 100 - Bincike

    Wani sabon bincike ya ce nan da shekara 100 mai zuwa, cutar sankarar bakin mahaifa za ta bace a fadin duniya.

    Kwayar cuta ta HPV ce ke jayo mafi yawan cutar, kuma ana iya yi mata riga-kafi.

    Binciken da aka buga a Mujallar Lancet Medical Journal ya ce daftarin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi na matakan shafe cutar daga doron kasa na iya kare rayuka miliyan sittin da biyu a shekaru 100 masu zuwa.

    Dole ne a tabbatar da cewa an gabatar da riga-kafin kwayar cuta ta HPV da gwaje-gwaje a bakin mahaifa da bayar da magunguna kafin a kawar da cutar.

    Tsarin na bukatar a yi wa kashi 90 na yara mata riga-kafin nan da shekara ta 2030.

  12. Kasashe Afirka sun dakatar da zuwa China, Saboda tsoron yaduwar Coronavirus

    Karin kasashen Afirka sun dakatar da tashin jiragensu zuwa China inda annobar Coronavirus ta kashe mutum 213.

    Ruwanda da Madagasca da Mauritius da Maroko sun dakatar da kamfanonin jiragen samansu daga zuwa China har sai abinda hali ya yi.

    Kamfanonin jiragen RwandAir da Air Madagascar da Air Mauritus da kuma Royal Air Maroc sun ce za su mayar wa fasinjojin da suka riga suka sayi tikitin zuwa China.

    A jiya Alhamis ne Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ayyana Coronovirus a matsayin babbar annoba a duniya, amma ta ce babu dalilin takaita harkokin kasuwanci ko tafiye-tafiye zuwa China.

    Kamfanin jiragen Ruwanda wato Rwanda ya dakatar da jiragensa daga zuwa birnin Guangzhou na China daga yau Juma'a.

    Royal Air Maroc na Maroko zai dakatar da zuwa China daga yau 31 ga watan Janairu zuwa ranar 29 ga watan Fabrairu saboda karancin fasinjoji daga Casablaca zuwa Beijing na China.

    Air Madagascar na gwamnatin Madagaska kuma daga gobe Asabar zai dakatar da zuwa Guangzhou a matsayin ''matakin rigakafi''.

    A kasar Mauritius kuma daga yau Juma'a Air Mauritius zai dakatar da tashi zuwa Shanghai amma zai ci gaba da zirga-zirga zuwa Hong Kong.

  13. Shekara 10 da rasuwar Maryam Babangida, Matan tsoffin shugabanni sun halarta

    An yi taron shekara 10 na tunawa da rasuwar matar tsohon shugaban Najeriya, Maryam Babangida, wadda ta fara rike ofishin uwargidan shugaban kasa a Najeriya.

    Uwargidan shugaban Najeriya Aisha Buhari tare da matan tsoffin shugabannin kasar sun halarci taron tunawa da marigayiyar, wato mai dakin tsohon shugaban mulkin sojin kasar Janar Ibrahim Badamasi Babangida IBB.

    Aisha Buhari ta bayyana farin cikin sake haduwa da matayen tsoffin shugabannin kasar a wurin taron inda ta ce sun tattauna abubuwa masu bayar da kwarin gwiwa.

    A lokacin mulkin mijinta ne marigayiya Maryam Babangida ta fara kirkiro da shirin tallafa wa mata.

    Sauran matan tsofaffin shugabannin da suka halarta sun hada da Mrs Fati Abdussalam Abubakar da Hajiya Turai 'Yar aduwa da kuma Dame Patience Goodluck Jonathan.

  14. EFCC ta saki Shehu Sani, Ya fito bayan shafe mako hudu a tsare

    Tsohon dan majisar dattawan Najeiya Sanata Shehu Sani ya fito bayan shafe mako hudu a tsare a hannun hukumar yaki da rashawa EFCC.

    Hukumar ta gurfanar da Shehu Sani a gaban wata babbar kotun da ke zamanta a Abuja bisa zargin zamba cikin aminci na dala 25,000, inda kotun ta bayar da belinsa.

    Shehu Sani ya musanta zargin da EFCC ke masa na karbar kudin daga hannun wani dillalin motoci.

    Sharudan belin da kotun ta ba shi sun hada da biyan naira miliyan goma sannan ya mika mata takardar fasfonsa.

  15. Takardar izini: Makarantu na kin daukan dalibai a Afirka ta Kudu

    Ana kin daukar yaran da ba su da takardun izinin zama a kasa shiga wasu makarantu a wasu yankunan Afirka ta Kudu.

    Rahoton hakan da wani shafin yada labarai a kasar RoundUp ya fitar ya ce hakan ya saba wa umurnin ma'aikatar ilimin kasar da ta ce a dauki yaran na wucin gadi a makarnatu kafin iyayensu su samu takardun izinin shiga kasar.

    Amma rahoton jaridar ya ambato kakakin ma'aikatar ilimin yankunan Western Cape da takwaransa Eastern Cape suna cewa neman takardun izinin zaman kasar ga dalibai a yankunansu ya saba doka.

    Afirka ta Kudu na yawan samun baki daga dadin nahiyar Afirka.

    Kashi 70 na bakin 'yan kasashen da ke makwabtaka da ita ne da suka hada da Zimbabwe da Mozambique da Lesotho.

  16. An gano makabartar da ta shekara 3,000, Akwai kayan gwalagwalai a makabartar ta manyan mutane

    Masu binciken tarihin kasu sun gano wata makabartar manyan mutane da ta shekara 3,000.

    Binciken ya hako akwatunan gawa 20 na dutse a makabartar da ake binne manyan malami da jami'an gwamnati shekara 3,000 da suka gabata.

    Daga cikin akwatunan gawan da suka hako har da wanda ake kebe wa Horun, wanda shi ne abin bautan masu bautar sararin samaniya.

    Sun kuma gano gumaka 10,000 da layu fiye da 700 da aka yi da zinare a makabartar da ke yankin Minya a birnin Alkahira na kasar Masar.

    Bayan haka sun gano wasu kaskuna da ake amfani da su waje ajiye kayan da ake amfani da su wajen adana gawa.

  17. Baki na yin katsalandan a Libya - MDD

    Majalisar Dinkin Duniya MDD ta ce katsalandan din kasashen ketare ke ci yi a a yakin basasan Libya ya saba wa yarjejeniyar da aka kulla a farkon wannan watan.

    Jakadan MDD a Libya Ghassan Salamé ya ce tsoma baki ba gaira ba dalili na iya kara rura wutar rikicin.

    Sai dai jami'in bai ambaci kasashen da yake zargi da saba ka'idar da aka kulla a birin Berlin na kasar Jamus ba.

    Amma Turkiyya da Fransa da Masar da wasu kasashe na daga cikin mahalarta taron.

    A baya-bayan nan Faransa ta zargi Turkiyya da yin kawo 'yan ina da yakin Syria zuwa Libya.

    Gwamantin Turkiyya na goyon bayan gwamnatin Libya mai hedikwata a birnin Tripoli.

    A nata bangaren, Turkiyya na zargin Faransa da goyon bayan 'yan tawayen da Janar Khalifa Haftar wajen yakar gwamantin da ke Tripoli.

  18. Ma'aikatan lafiya na cikin damuwa a Najeriya, Suna fama da rashin kayan aikin Coronovirus inji kungiyarsu

    Ma'aikatan lafiya a Najeriya sun nuna damuwa game da matakan da kasar ke dauka kan annobar Coronavirus, duk da tabbacin da gwamnati ta bayar na shirin tunkarar bullar cutar.

    Kungiyar ma'aikatan jinya da ungozomomi NANNM ta ce ma'aikatan jinya a kasar na fama da karancin kayan gudanar da ayyukan du suka danganci kwayar cutar.

    Jaridar Punch ta ruwaito shugaban kungiyar Abdulrauf Adeniji na cewa ba a tanadar wa malaman jinyan isassun kayan kariya ba.

    Hakan ya sa suke samar wa kansu kayan kariya domin yin aikin tantance cutar a tashoshin shigowa da fita daga kasar.

    Amma a baya ministan lafiya Osagie Ehanire ya ce a shirye ma'aikatarsa take domin tunkarar barazanar bullar annobar kuma ma'aikatar lafiya na tantance fasinjoji a tashoshin jiragen kasar.

    Ya zuwa yanzu gwaje-gwaje da aka gudanar sun tabbabar da cewa dukkan mutanen da ake zargi na dauke da kwayar cutar a nahiyar Afirka ba sa dauke da ita.

  19. Kenyan ta dakatar da zuwa Guangzhou

    Kenya ta dakatar da zirga-zirgar kamfanin jiragen samanta zuwa yankin Guangzhou na China saboda annobar cutar Coronavirus.

    Annobar Coronavirus ta yi ajalin mutu 130 a China yayin da ta watsu zuwa waasu kasashe 16.

    Jiragen kamfanin Kenyan Airways kan yi sawu shida tsakanin birnin Nairbobi zuwa Guangzhou a kowane mako.

    Ana zargin wasu mutum shida a Afirka na dauke da cutar, cikinsu har da 'yan kasar Kenya.

    Ma'aikatar lafiyar Kenya ta ce ta karbo sakamakon gwajin da aka yi na wadanda ake zargi na dauke da kwayar cutar Corovirus.

    Ta ce sakamakon gwajin da aka gudanar a Afirka ta Kudu ya tabbatar da cewa mutanen ba sa dauke da kwayar cutar.

  20. 'Yan Democrat na fuskantar koma baya kan tsige Trump

    'Yan jam'iyyar Democrat a Amurka sun fuskanci babban koma baya a bukatarsu ta kiran shaidu a sauraren karar tsige Shugaba Trump.

    Sun bukaci 'yan Republican hudu su mara masu baya, a kara bai wa wani shaida damar bayar da bayanai, amma daya daga cikin sanatocin da a baya yake inda-inda ya ce yanzu ba zai mara masu baya ba.

    Lamar Alexander ya ce babu bukatar karin shaidu da za su tabbatar shugaban bai aikata laifin da za a iya tsige shi ba.

    'Yan Democrat sun so musamman su ji daga bakin tsohon mai bai wa Shugaba Trump shawara kan harkokin tsaro, John Bolton.

    Rahotanni sun bayyana cewa ya ce shugaban ya taba gaya masa baki da baki cewa ya dakatar da bai wa Ukraine agajin soji har sai ta amince ta yi bincike kan abokin hamyyarsa, Joe Biden.