Abubuwan da suka faru a Najeriya da makwabtanta

Shafi ne da ke kawo maku abubuwan da suke faruwa a Najeriya da Nijar da Ghana da kuma Kamaru, har ma da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Halima Umar Saleh and Umar Mikail

  1. An kama basarake a Kaduna kan zargin aiki da masu garkuwa

    Rundunar 'yan sandan jihar Kaduna ta ce ta kama wani basarake a jihar bisa zarginsa da yin aiki da masu satar mutane don neman kudin fansa.

    Basaraken dai na cikin mutum 39 da rundunar ta yi holinsu a yammacin jiya Alhamis.

    Kaduna na cikin jihohin Najeriya da suka fi fama da matsalar masu satar mutane domin neman kudin fansa.

    A baya-bayan nan ma sai da dangin wani shugaban makarantar firamare a yankin Birnin Gwari suka ce masu garkuwar sun kashe dan'uwansu duk da kudin fansar da suka harhada suka kai masu.

    Nabila Muktar Uba ta tattauna da DSP Yakubu Sabo, mai magana da yawun rundunar 'yan sandan jihar Kaduna. Saurari hirar a kasa:

    Bayanan sautiTattaunawa da DSP Yakubu Sabo
  2. Najeriya za ta mayar da abubuwan tarihi gida

    Gwamnatin Najeriya ta kaddamar da wani gangamin karbo wasu kayayyakin tarihin kasar da wasu kasashe suka yi kodai fasakaurinsa ko awon gaba da su.

    Ya kuma ce gwamnati ta yi farin ciki da samun tayi daga wasu kasashen cewa za su mayar ma ta da kayan tarihin.

    Lai
  3. Masana sun soki bukatar Buhari ta neman bashi

    Masana tattalin arziki a Najeriya na cigaba da tofa albarkacin bakinsu kan bukatar da shugaban kasar Muhammadu Buhari ya mika wa majalisar dokokin kasar, ta neman ciyo bashin dala biliyan 30, kwatankwacin naira tiriliyan 10 a kudin kasar.

    Dr Shamsuddin Muhammad wanda malami ne a sashen nazarin tattalin arziki na jami’ar Bayero da ke Kano, ya ce ya yi mamaki kwarai da shugaban kasar Muhammadu Buhari ya sake aika wa majalisar wannan bukata a karo na biyu.

    Buhari
  4. 'Yan majalisar kasashen Afirka za su gana kan zaman lafiya a Nijar

    'Yan majalisar Najeriya

    Asalin hoton, @NigSenate

    Yayin taron zaman lafiyar yake gudana a birnin Yamai na kasar Nijar, a yau ne 'yan majalisa sama da 120 da suka fito daga kasashe daban-daban na Afrika ke wani zama tare da takwarorinsu na Majalisa Dokokin Nijar.

    Za su yi taron ne domin tattauna muhimman batutuwa da suka hada da na zaman lafiyar.

    A baya-bayan nan kasar Nijar ta fuskanci hare-haren 'yan bindiga, inda suka kashe sojoji kusan 12 sannan kuma suka kona makarantiu a lokuta mabambanta.

  5. Ciyo Bashi: Sanatoci na muhawara kan bukatar Buhari

    Bukatar da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sake tura wa majalisar dattawa domin ta amince ya ciyo bashi na ci gaba da jawo.

    Sanata Shehu Sani, wanda tsohon sanata ne a majalisa ta takwas wadda ta dakile kudirin na Shugaba Buhari karkashin jagorancin Bukola Saraki, ya ce sun yi hakan ne saboda kada Najeriya ta koma cikin kangin bashi.

    Sai dai Sanata Sahabi Ya'u, mataimakin mai ladabtarwa a bangaren marasa rinjaye a Majalisar Dattawa, ya ce Buhari ya riga ya karbo bashin, kawai dama yake nema daga majalisar domin ya yi amfani da shi.

    Buhari ya sake tura bukatar neman karbo bashin kusan dala biliyan 30 bayan ya fuskanci tirjiya a majalisa ta takwas a karkashin jagorancin Bukola Saraki.

    Saurari tattaunawar sanatocin biyu da wakilanmu:

    Bayanan sautiSanata Shehu Sani kan bukatar ciyo bashi
    Bayanan sautiSanata Sahabi Ya'u kan bukatar ciyo bashi
  6. Barka

    Masu bibiyarmu barkanku da safiyar Juma'a.

    Ku duba kasa domin karanta labaran ranar Alhamis.

  7. Buhari ya bukaci majalisa ta ba shi damar karbo bashi

    Shugaba Muhammadu Buhari

    Asalin hoton, Nigeria Presidency

    Shugaba Muhammadu Buhari ya nemi Majalisar Tarayya ta sake dubawa tare da sahhale kudirin neman bashin da ya aika wa majalisa ta takwas mai suna 2016-2018 External Borrowing Plan.

    Shugaban ya gabatar da bukatar ne a wata wasika da ya aike wa 'yan majalisar kuma aka karanta ta a yau Alhamis a zauren majalisar.

    Buhari ya bayyana a cikin wasikar cewa za a karbo bashin ne saboada kammala wasu ayyuyka da aka zayyana a cikin kudirin neman bashin na shekarar 2016-2018.

    Ya kuma yi bayanin cewa majalisa ta takwas, karkashin jagorancin Abubakar Bukola Saraki, wani bangare kawai na dokar ta amince da shi, "abin da ya kawo tsaiko ga wasu daga cikin ayyukan raya kasar da gwamnatinsa ke yi," in ji Buhari.

    Shugaban ya ce ayyukan da rashin amincewa da kudirin ya shafa sun hada da hakar ma'adanai da wutar lantarki da lafiya da noma da ruwan sha da kuma ilimi.

    "Saboda haka na hado maku da kwafin bayanai daga Ministar Kudi da Tsare-Tsare game da ayyukan da muke bukatar gudanarwa idan kuka amince da kudirin 2016 – 2018 External Borrowing."

  8. EFCC ta kama Ibrahim Magu na boge

    Hukumar yaki da cin hanici da yi wa tattalin arzikin kasa ta'annati a Najeriya EFCC ta ce ta cafke wani mutum da yake sojan-gona a matsayin shugaban hukumar wato Ibrahim Magu.

    Ofishin hukumar na garin Fatakwal ne ya cafke "Ibrahim Magu" a ranar Laraba, kamar yadda ta sanar a shafinta na Twitter.

    "Yana amfani da sunan ne wajen zambatar jama'a tare da bata sunan wasu manyan jami'an hukumar raya yankin Niger Delta ta NNDC," in ji EFCC.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  9. Za a yi taron zaman lafiya da tsaro na Afirka a Nijar

    Jamhuriyar Nijar za ta karbi bakuncin taron Nahiyar Afirka kan Zaman Lafiya da Tsaro a ranar Alhamis ta mako mai zuwa, inda mahalarta 2,000 za su je.

    Shugaba Mahamadou Issifou ne shugaban taron mai taken ''Gina Afirka mai zaman lafiya da hadin kai da tsaro da sasantawa da ci gaba.''

    Taron zai samu halartar tsofaffin shugabannin kasashen Afirka da wadanda ke kan mulki da sanatoci da shugabannin manyan cibiyoyi.

    Za a shafe kwana biyu ana gudanar da taron a Niamye, babban birnin Nijar.

    Nijar President

    Asalin hoton, Getty Images

  10. Gwamnatin Sokoto ta yi wa ma'aikatan boge 8,000 afuwa

    Tambuwal

    Gwamnatin jihar Sokoto ta yi wa ma'aikatan boge 8,000 da masu karbar albashin da bai dace ba afuwa.

    Kwamishinan kudi na jihar Alhaji Abdussamad Dasuki ne ya bayyana hakan a wani taron manema.

    Ya ce an yi hakan ne don ma'aikatan gwamnatin da suke karbar albashin da ba halalinsu ba ko suke abubuwn da ba su dace ba da su samu kwarin gwiwar bayyana kansu ga gwamnati ba tare da al'umma sun sani ba don samun afuwar gwamnati.

    Za a rufe karbar afuwar ne a ranar 9 ga watan Disambar 2019.

  11. Shugaban Ghana ya bai wa 'yan kasashen waje 126 takardun zama 'yan kasa

    Ga hotunan yadda taron bayar da takardun zama 'yan kasar ya kasance:

    Ghana diaspora
    Ghana diaspora
    Ghana diaspora
    Ghana diaspora
    Ghana diaspora
    Ghana diaspora
  12. 'Yan kasashen waje a Najeriya sun koka kan rajistar sunayensu

    Hukumar shige da fice ta Najeriya

    Asalin hoton, @nigimmigration

    'Yan kasashen waje mazauna Najeriya na korafi kan aikin rajistar tantance su da hukumar shige da fice ke yi.

    Tun kafin fara aikin rajistar ne hukumomin shige da fice na kasar suka sanar da cewa kyauta za a gudanar da aikin rajistar kuma ga dukkanin 'yan kasashen waje da ke zaune a fadin Najeriya.

    Mazauna wasu jihohin kasar sun koka kan yadda suka ce ma’aikatan da ke aikin rajistar sun bukaci su biya kudi kafin a shigar da sunayensu.

    Ga rahoton Abdou Halilou:

    Bayanan sauti'Yan kasashen waje a Najeriya sun koka kan rajistar sunayensu
  13. Ana tuhumar maza da mata 57 da laifin luwadi a Legas

    A Najeriya wata babbar kotun tarayya a Legas ta fara shari’ar matasan nan maza da mata 57 da aka kama suna masha’a a wata maboya cikin wani otal da ke wajen birnin Legas.

    Ana zargin mazan da neman 'yan uwansu maza, haka ma matan ana zarginsu da yin madigo, zargin da dukkaninsu suka musanta.

    Ga rahoton da Umar Shehu 'Yanleman ya hada mana daga Legas din.

    Bayanan sautiAna tuhumar maza da mata 57 da laifin luwadi a Legas
  14. Kungiyar Tarayyar Afirka da Commonwealth na son kawo karshen rikicin Kamaru

    Kungiyoyin Tarayyar Afirka da na Commonwealth da Francophonie sun ce za su yi iya kokarinsu na ganin sun kawo karshen rikicin da Kamaru take fama da shi ta yankin rainon Ingila.

    Kungiyoyin sun bayyana hakan ne bayan sun gana da shugaban kasa Paul Biya da wasu shugabannin jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen hula.

    Har a yanzu wutar rikici na dada ci gaba da ruruwa a yankin rainon Ingila tsakanin masu fafutuka na Ambazonia da jami’an tsaro na Gwamnati.

    Dukkansu na kashe juna.

    Lamarin kuma na shafar fararen hula. Shugaban kasa wanda shi ne ya shirya babbar muhawar ta neman sulhunta rikicin watanni biyu kenan da suka gabata, bai bayar da izinin fara aiwatar da matakan da aka dauka ba.

  15. 'Yan Ghana 100 za su je Barbados yin aiki

    Ma’aikatar lafiya a Ghana ta dauki ma’aikatan jinya sama da 100 da za su je yin aiki a kasar Barbados.

    Hakan ya biyo bayan rokon da Firai Ministar Barbados, Mia Amor Mottley ta yi yayin wata ziyara da shugaban kasar Ghanan Nana Akufo-ADDO ya kai kasar da ke yankin Caribbean a watan Yuni.

  16. 'Abinci ya kara tsada saboda rufe iyakokin Najeriya'

    Zainab Shamsuna

    Asalin hoton, Zainab Shamsuna Twitter

    Gwamnatin Najeriya ta amsa cewa rufe iyakokin tudu na kasar ya taimaka wajen karuwar hauhawar farashin kayayyaki da ake fuskanta.

    A cewar alkaluman baya-bayan nan daga Hukumar Kididdiga ta Najeriya, alkaluman hauhawar farashin ya kai kusan kashi 12 a watan Oktoba.

    Ministar kasafin kudi da tsare-tsare ta kasa, Hajiya Zainab Ahmed Shamsuna ce ta bayyana hakan yayin amsa tambayoyin manema labarai bayan taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya, cewa an samu karin hauhawar farashin kayan abinci ne sakamakon rufe kan iyakoki.

    A ranar 21 ga watan Agusta ne Najeriya ta rufe iyakokinta na kan tudu ba tare da wani gargadi ba - a cewarta don shawo kan gagarumin fasa-kwaurin kayayyaki musamman ma dai shinkafa zuwa cikin kasar.

    Bayanan sautiKalaman minsitar kudi kan tsadar abinci saboda rufe boda
  17. Barka

    Masu sauraro barkanmu da sake saduwa da ku a wannan safiya ta Alhamis.

    Ku biyo mu a wannan shafi don jin abubuwa da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da sauran makwabta.

  18. Majalisar dokokin jihar ta yi magana kan soke sabbin masarautun Kano

    A karon farko majalisar dokokin jihar Kano a Najeriya ta mayar da martani kan hukuncin da wata kotu ta yanke kan wata doka da majalisar ta yi na kirkiro sababbin masarautu hudu a jihar.

    Martanin majalisar Kanon na zuwa ne kwana biyar bayan hukuncin da kotun ta yanke, sannan kuma a dai-dai lokacin da ake rahotanni ke cewa majalisar za ta sake gabatar da kudurin samar da dokar kirkiro masarautun.

    Shugaban masu rinjaye na majalisar ta dokokin Kano, Labaran Abdul-Madari ya bayyana cewar suna ci gaba da tattaunawa da lauyoyinsu da kuma bangaren gwamnati domin samar da matsaya.

    Sai dai ya musanta cewa yanke hutun da suka yi na da alaka da batun sabbin masarautun.

    ''Maganar gaskiya ba abin da ya dawo da mu kenan ba, saboda shi wannan batu yana gaban kotu kuma lauyoyinmu suna tattaunawa da juna domin cimma matsayar daukaka kara ko akasin hakan.

    Amma a yanzu ina shaida ma ka batun da ya dawo da mu daga hutu shi ne na ilimi, ban sani ba ko zama na gaba za a tattauna a kai amma a yanzu babu wannan maganar sam.''

    Sarki Sanusi

    Asalin hoton, Getty Images

  19. Matawalle ya ce zai yi amfani da kudin tsoffin gwamnoni wajen raya kasa

    Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya ce zai yi amfani da fanshon tsoffin gwamnoni da ya soke wajen raya karkara.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin ya fitar, gwamna Matawalle ya yi takaicin yadda tsohon gwamna ya ke neman a biya shi makudan kudade a dai-dai lokacin da sauran 'yan fansho a jihar ke cikin kangin wahala saboda rashin biyan su kudadensu.

    Ya kara da cewa 'yan fansho na bin gwamnatin da ta shude bashin kudade da suka kai naira bilyan 10.

    Matawalle
  20. CISLAC ta yaba wa Bello Matawalle

    Kungiyar mai fafutukar yaki da rashawa da cin hanci a Najeriya, CISLAC ta ce matakin da gwamnan jihar Zamfara ya dauka na soke dokar da ta amince a bai wa tsoffin gwamnoni da mataimakansu fansho abun a yaba ne.

    A wata sanarwa da shugaban kungiyar a Najeriya, Auwal Musa Rafsanjani ya yi kira ga shugaba Buhari da ya yi koyi da jihar ta Zamfara wajen ganin an rage kashe kudaden gwamnati.

    Kungiyar ta kuma nemi sauran gwamnonin jihohi da su yi koyi da gwamnan na Zamfara.

    Matawalle ya soke dokar da ta bai wa tsaffin gwamnoni fansho