An tsaurara matakan tsaro a sassan Uganda gabannin zaɓe

Asalin hoton, Reuters
Kwanaki biyar gabanin zaɓen Uganda, an jibge tarin jami'an tsaro a Kampala babban birnin ƙasar.
A sassa daban-daban na birnin, an ga jami’an tsaro na yin jerin gwano, yayin da motocin sulke ke girke a wurare daban-daban.
Muƙaddashin daraktan yaɗa labarai na rundunar sojin Uganda, Kanar Chris Magezi, ya wallafa wani bidiyo a shafinsa na X da ke nuna jami’an soji na sintiri a cikin birnin a cikin motoci masu sulke.
"Babu wani dalili na fargaba. Duk da haka, ba za mu lamunci barazanar tashin hankali a lokacin zaɓen daga wasu ƴan siyasa da magoya bayansu ba," Col. Magezi ya rubuta a shafinsa na X.
Galibi zaɓuɓɓukan ƙasar Uganda na baya sun zo da tashe-tashen hankula, waɗanda yawanci suka kasance here-here kan ƴan adawa da magoya bayansu.
A farkon makon nan ne mai magana da yawun ƴan sanda Kituuma Rusoke ya musanta zargin cewa jami’an tsaro na yiwa ƴan siyasan adawa da magoya bayansu barazana.
Sama da masu kaɗa ƙuri'a miliyan 20 ne ke shirin fitowa rumfunan zaɓe a mako mai zuwa, a ranar 15 ga watan Janairu, domin zaɓen shugaban ƙasa da ƴan majalisar dokoki.

















